Northern Nigeria (Arewa): Breaking News In Nigeria | Inside Arewa Blog Politics | Entertainment News |Fictional Stories | Lifestyle.
Wednesday, 30 October 2019
FG to ASUU: No going back on IPPIS platform
Monday, 11 June 2018
An Nemi Buhari Ya Binciki Yadda Obasonjo Ya Mikawa Kamaru Yankin Bakassi
An Nemi Buhari Ya Binciki Yadda Obasonjo Ya Mikawa Kamaru Yankin Bakassi
Tsohon Gwamnan Abia, Orji Uzor Kalu ya nemi Shugaba Muhammad Buhari kan ya binciki Cif Olusegun Obasonjo game da yadda ya mikawa Kasar Kamaru yankin nan mai arzikin man fetur na Bakassi .
Tsohon Gwamnan ya ce, akwai wata manufa ta biyan bukata kansa idan aka yi la'akari da yadda Obasonjo ya mika yankin cikin sauki ba tare da wata jayayya ba.
Wednesday, 6 June 2018
Buhari Ma Ya Ci Kudin Makamai, Cewar Sule Lamido
...idan Buhari ya kama Jonathan sai sama ta fado, cewarsa
Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Dakta Sule Lamido ya zargi shugaban kasa Muhammadu Buhari da cewa shi ma yaci kudin makamai.
Lamido ya bayyana haka ne a shafinsa na kafar sadarwar zamani, Facebook, inda yace tsohon mai baiwa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan shawara kan harkokin tsaro, Kanau Sambo Dasuki ya baiwa Buhari motoci masu sulke guda biyu bayan da Boko Haram ta kai masa hari a Kaduna.
Haka kuma Sule Lamido ya kara da cewa me ya sa Buhari ya gagara kama Jonathan, bayan duk wadanda ake tuhuma suna na da nasaba da tsohon shugaban?
“Wai a ina Dasuki ya samu dala biliyan 2.5 da ya rarrabawa manyan mutane yayin da ake gab da zaben 2015, laifin da ya sa har yanzu yake daure a hannun hukumar DSS? A ina Nenadi ta samu makudan bilyoyi da ta rarrabawa jihohi wanda ya sa a yanzu haka take gaban Kotu?
“Ga amsa, dukkaninsu sun samu kudaden ne daga babban bankin Nijeriya dake karkashin shugaban bankin na yanzu, Godwin Emefeile, kuma tsohon shuhgaba Jonathan ne ya bada wannan umarni", cewar Lamido.
Daga karshe Sule Lamido wanda yake takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP yace: “Don haka tunda Alkali Binta Nyako ta yanke hukucin cewar bai kamata a kama duk wanda aka basu umarnin yin laifi ba, Gwmanatin Buhari ba zata iya kama Jonathan bane, ta gwada mu gani, da sai sama ta fado".
Tuesday, 5 June 2018
Tsuguno bata karewa Dino Malaye ba za'a cigaba da gurfanar dashi gaban Kotu
Tunda Dino Melaye ya samu lafiya, a cigaba da gurfanarsa – AGF Malami ya bukaci kotu
Naijdotcom ta ruwaito Ministan Shari’a kuma babban lauyan tarayya, Abubakar Malami, ya bukaci babban kotun birnin tarayya Abuja, da ta cigaba da gurfanar da Sanata Dino Melaye, bayan dakatad da sanadiyar jinya da yake yi.
Jaridar Punch ta bada rahoto a jiya Litinin cewa ta samu wasikan da aka turawa kotu tana sanar da ita cewa Dino Melaye ya samu lafiya har ya koma bakin aiki a majalisar dattawa ranan30 ga watan Mayu.
Ofishin babban lauyan kasa tana tuhumar Dino Melaye da karya ga hukumar yan sanda domin yiwa na kusa da gwamnan jihar Kogi, Edward Onoja David, sharri cewa ya tura wasu kashe shi.
A ranan 17 ga watan Mayu 2018, Justice Olasunbo Goodluck, ya dakatad da karar Melaye ne zuwa lokacin da za’a sallameshi daga babban asibitin tarayya da ke Abuja inda yake kwance.
A wasikar, lauyan gwamnati, Mr Shuaibu Labara, ya laburtawa kotu cewa an salami Melaye kuma ya koma bakin aiki rike da sanda da abu a wuya.
Tunda ya koma kuma, an ganshi yana magana a majalisa saboda haka, kotu ta bada sabon ranan domin cigaba da gurfanarsa.
Monday, 28 May 2018
NI ISIYAKU ORIS DA DAUDA RARARA MU MUKA JE MUKA KARBO NERA MILYAN 100 A HANNUN ABDULAZIZ YARI
Daga JARIDAR DIMOKURADIYYA:
Matemakin shugaban kungiyar mawaka Ibrahim Yala yace Isiyaku Oris ya tabbatar mishi da cewar Gwamnan Jihar Zamfara AbdulAziz Yari nera Milyan 100 ya baiwa Dauda Rarara ba nera milyan 60 ba.
Isiyaku Oris wanda tare suka je Wajen Gwamnan Jihar Zamfara kuma shima yana daya daga cikin mawakan kungiyar yace tabbas an baiwa Rarara kudin kungiya kuma suna hannun shi nera milyan 100.
Ibrahim Yala Wanda shine matemakin shugaban kungiyar mawaka yace yanzu idan suka kira Dauda Rarara a waya baya dauka saboda maganar kudade "kuma tun lokacin da Rarara ya bukaci mu hada wannan kungiyar na gane cewar so yake yayi amfani damu; Motocin kungiyar mu duka suna hannun shi yana ta amfani dasu.
Tunda farko shugaban kungiyar Haruna Aliyu Ningi yace Rarara yace mishi nera milyan 60 kawai aka bashi kuma daga ciki milyan sittin din ya baiwa wadanda suka yi hanya kudaden suka fito nera milyan 18, kuma ragowar nera milyan 42 da suka rage suna akawut dina kuma akawut din ya sami matsala.
To amma yanzu an tuntubi Dauda Rarara yace shi bai ma san da maganar wasu kudade ba.
Dauda Rarara a wata hira da yayi da wani Danjarida yace shi babu wanda ya bashi ne goma.
Thursday, 24 May 2018
An bukaci Shugaba Buhari ya cunawa Obasanjo da Jonathan hukumar EFCC
Wata kungiya mai zaman kanta a Najeriya dake rajin kare martabar dan adam da kuma tabbatuwar demokradiyya watau Socio-Economic Rights and Accountability Project (SERAP) a turance ta bukaci gwamnatin tarayya da ta soma binciken tsaffin shugabannin kasar Najeriya game da yadda suka tafiyar da harkar wutar lantarkin kasar.
SERAP a cikin wata sanarwa da ta fitar ta rabawa manema labarai, ta bayyana cewa abun takaici ne a kashe kusan dalar Amurka biliyan 16 a harkar wutar lantarkin amma har yanzu ba ta canza zane ba.
Daga nan sai kungiyar ta shawarci shugaban kasar da ya mika tsaffin shugabannin kasar ga hukumomin binciken da suka kamata domin gudanar da bincike a kan su.
EFCC Ta Sake Kama Shekarau
▪ Gobe Za A Gurfanar Da Shi Gaban Kotu
Rahotanni daga Kano sun tabbatar da cewa a halin yanzu Tsohon Gwamnan Kano, Ibrahim Shekarau yana tsare a ofishin hukumar EFCC da ke jihar Kano.
Daruruwan magoya bayan Shekarau ne dai suka yi cincirindo a titin Dandalin mahajjata inda suka yi kokarin hana tsohon gwamnan shiga ofishin EFCC wanda ya isa wurin da misalin Karfe hudu na Yamma, lamarin da ya janyo aka karo jami'an tsaro wadanda suka yi amfani da borkonon tsohuwa wajen tarwatsa magoya bayan Shekarau.
A gobe Alhamis ne dai, hukuma za ta gurfanar da tsohon Gwamnan a gaban kotun tarayya da ke Kano shi da Aminu Wali da Mansur Ahmed bisa laifin karbar Naira Milyan 950 daga hannun Tsohuwar Ministar Mai, Alison Deizani Madueke a lokacin zaben 2015. Sai dai Kakakin Tsohon Gwamnan, Sule Sule ya nuna cewa an tuhumi Shekarau ne saboda ya caccaki gwamnatin Shugaba Buhari.
Tuesday, 22 May 2018
EFCC Ta Kama Tsohon Dan Takara Gwamnan Jihar Sokoto Da Tsohon Ministan Ruwa Da Wasu 3
EFCC Ta Kama Tsohon Dan Takara Gwamnan Jihar Sokoto Da Tsohon Ministan Ruwa Da Wasu 3
DAGA CMRD A'B ZUBAIRU
Hukumar EFCC ta kai wa wasu jiga-jigan jam'iyyar PDP samame a jihar Sokoto bisa zargin su da karba 500,000000 a shekarar 2015.
Wednesday, 16 May 2018
Mutane Ba Su Da Amana A Yau — Buhari
▪Ba Buhari Kadai Ba Ne Mai Gaskiya — Dogara
Shugaba Muhammad Buhari ya bayyana cewa a yau mutane ba su dauki cin amana a matsayin laifi ba a maimaikon haka rashin amana ya zama wata dabi'a a tsakanin al'ummar.
Buhari ya yi wannan ikirarin ne a lokacin da bude sabon hedkwatar hukumar EFCC inda ya ce yaki da rashawa na da matukar wahala saboda ya shafi rassa daban daban na rayuwar al'umma.
A nasa bangaren, Shugaban Majalisar Wakilai, Yakubu Dogara ya yi ikirarin cewa har yanzu akwai milyoyin 'yan Nijeriya wadanda ke da gaskiya da rikon amana ba ya ga Shugaba Muhammad Buhari.
Monday, 30 April 2018
A Karshe Kotu Ta Damka Wasu Gidajen Patience Jonathan Ga Gwamnati
Wata kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta damkawa gwamnatin tarayya wasu gidaje guda biyu mallakar Uwargidan Tsohon Shugaban Kasa, Patience Jonathan.
Thursday, 19 April 2018
Rundunar 'Yan Sandan Neja Ta Kama Gaggan Barayin Da Suka Addabi Jihar

Saturday, 31 March 2018
An Kama Barayin Shanu A Jihar Taraba
Thursday, 22 February 2018
Corruption Getting Worse In Nigeria’ — Transparency International Releases 2017
Sultan: Corruption At A Very High Level In Nigeria… Things Are Not Okay
Sa’ad Abubakar III, the sultan of Sokoto, has lamented that corruption is at a “very high level” in Nigeria.
“Things are bad,” the monarch said while adding that Nigerians must fight the scourge of corruption to a “terminal end”.
The sultan made the remark on Wednesday while speaking at the public presentation of ‘Dynamics of Revealed Knowledge and Human Sciences’, a book written in honour of Ishaq Oloyede, registrar of the Joint Admissions and Matriculation Board (JAMB).










