Showing posts with label Hausa Novels. Show all posts
Showing posts with label Hausa Novels. Show all posts

Sunday, 24 September 2017

Love and its Destiny Episode Five


Read other Inside Arewa Story:  
First of all I will like to say thank you to all of http://www.insidearewa.com and http://www.insidearewa.com.ng readers for the journey so far. Thank you for supporting me and thank you for everything I really appreciate you. Remember to always visit the site. Long live Arewa and long live Nigeria.
Note: Date of sharing next episode may change due to the nature of my work so no fix date but I’ll keep to my words Insha Allah on any date fix for new episode. Enjoy your reading and follow us on all social media @Insidearewa

Sunday, 14 August 2016

Halaccin Sarauta Final Episode.

Hallaccin Sarauta Previous Episode

Zamu Fara sabon Littafi Wednesday Insha Allah.

Sunyi kokarinsu don ganin sunsamu laya kowani abu makamancin haka don samun babban kyauta kamar yadda aliya tamusu alkawari, basu sami komi ba haka suka hakura har dare ana abu daya, aliya duk tashiga damuwa da tashin hankali, anki abarta tahuta da mijinta ankuma ki abarta tazauna lafiya, Daredare takaranta surorin kamar yadda akace tayi takwanta zuciyanta cike da son kama kowacece, acan tafarajin kukan kulya da kare nan da nan tafara Allahumma ajirni fi musibati waakrijhi khailriha, tanayi tana hadawa da auxubillah, ahaka tazauna yusuf na gefenta yana tayata addua yagagara bacci duk da taso yayi anma yaki, hakan yasa suka zauna suna ta addua ahaka har asuba, asuba nayi yafice masallaci itama tayi sallolinta sannan tawuce kan gado , tana addua harta jira bacci ya kwasheta Tayi dan mafarkan Allah kuma yabata nasara ta jiwa kuran ciwo, itama ta ji ciwo bata tashiba sai karfe daya. Inda tayiwa yusuf bayani yace tacigaba dahaka har na sati kamar yadda malamin yace zata kashe kuran inhar tana kokarin fada dashi.

kullum tana fada dashi kuran yadawo baida ishashen karfi, aranan tafito tana son zuwa fannin yakolo ko zasu gaysa, wani bakin abu tagani rana ya hasko mata, harta wuce takoma tadauka ga mamakinta laya ne, hannunta na bari tadauka tana addua, harta isa dakinta tana isa tanemi babban container tazuba sannan tarufe, wayanta tadauka takira yusuf yana dauka muryanta na rawa tace "kayi sauri kazo gyda, don Allah kayi sauri" yadda yaji magananta tuni ya tsure dama yashiga kasuwa ne babu shiri yadawo fada, tana zaune a falo yashigo anan tanuna masa shima ya mugun tsorata anma dole yadanne nasa don karta rude, wurin malamin suka nufa dashi, yadauki layan sannan yace tayi addua ta tofa ajikinta ta kona layan agun, aikuwa tana haka yace toh yanzu saura takarasa nakasa kuran inhar tayi haka toh ba tabbas wacce tamata wannan sihirin, asiranta zai tonu dahaka sukayi sallama dashi. Sunkoma gida sukaga fannin falmata a cike arude yusuf yashige aliya na biye dashi abayanta, falmata ce adaki tana kwance sai kuyangu akanta, dakuma yakolo su umma uwar soro, mutane dayawa dai haka, hankalinshi tuni yafara tashi, yaleka ta dakyau ga mamakinsa ganinta yayi kaman ba itaba, kamanninta duk yacanja, tacanja wasu manyan kuraje ne suka fito mata, ga doyi kuma, kowa hannu na hanci tuni yakai nashi hannun , anan akace kowa ya watse aka barsu kadai adakin umma uwar soro tace takai awa daya ahaka, don tunda jakadiya tazo tamusu bayani akan falmata nakwance kawai saiga kurajen sunfara fitowa abun kuma bai tsayaba, shiru yayi zuciyarsa na masa zargi, anma duk dahaka yazauna, duk iya kokarin da akayi dawasu likitoti abu yaki tafiya wari yaki tsayawa, falmata acikin dakikai kadan tadawo abun tausayi, wanda hakan tuni yafara yawo a fada, falmata tayi sihiri yadawo kanta acewarsu kenan, kowa sai Allah kara yake, dama ta addabi kowa acikin fadan, kowa yanata farinciki, yayan cikinta ne kawai suke kukan abun, suma ni benaxir na tabbata don ita tahaifesu shiyasa, inbahaka ba babu yadda zaayi suji haushin abunda yake samunta, yusuf dai zama yayi agefenta yana kallonta yarasa ma yazaiyi sannan kuma mezaice mata.

Dahaka tana kallonshi tana zubda hawaye, aliya ma tana daga gefe tayi tagumi duk tsanar falmata datayi yaukuma tausayinta taji, tamike tadauko ruwa sannan tabata, tana jingine a kujera, tana kallon aliya yusuf ma nagefe, Wani abun mamaki shine tun ranan aliya tadena jin kukan kare da kulya, sannan tafara baccinta abun ya matukar bata mamaki hamdallah tarinkayi wa Allah tana godiya, tayi salollinta, Falmata ankaita asibiti anma sunbada shawaran ayi maganin gida nan da nan aka nemo mai maganin gargajiya, yusuf kuwa yahado da wannan malamin bayan dan magana dasukayi sai malamin yace mishi tabbas itace, yusuf jikinshi yayi sanyi donhaka dakyar yakira aliya malamin itama yamata bayani kuka tayi sosai jikinta yayi sanyi, tanata tunani duniyan shinawa yake? Da girmanka da mutuncinka zaka nemi gun boka , me boka zaimaka wanda Allah baimaka ba? Mezaka tanadar wa kanka agun boka? Daya wuci wulakanci da dizgi, duniyar kanta nawa take da mutum zai sa rayuwarshi ta kaskance, ta zama wulakantacce, Takoma gun falmata anma bata canja mata fuska ba, tacigaba da zama tana jinyarta da bayin dasukenan, Wannan hali na aliya yasaka falmata jin kunya, taji inama tunfarko bata kullaceta ba, bata mata asiriba, sannan bata musguna mata ba, tana kuka taroki gafaran aliya takuma nuna nadamarta a fili, aliya tanuna mata bakomi hakan yasa tacire komi aranta, mijinta kuwa tuni tasamu kanshi duk da dafarko yana fushi da halin mahaifiyarsa aliya tayi iya kokarinta ta gwada masa muhimmancin mahaifiyarsa dakuma hatsarin fushi da ita, tabbas yayi alfahari da aliya domin kuwa tazamto masa garkuwa, itace macen da annabi yace a aura wacce zata gyra maka yayinda kashiga hatsari wacce zata zamo maka garkuwa,yana alfahari da aliya yana kuma tausayinta a matsayin marainiya.

Falmata ahankali tafara samun sauki da yusuf yahado malamai anata addua da saukan qurani, domin sarkin yayi tashi harya gaji, Allah cikin ikonsa tasamu sauki duniya takoya mata hankali ta nutsu tazama mutumiyar arziki domin kuwa hatta bayi darajasu take, kansu yazama ahade da yakolo Yayinda aliya tahade da mijinta, abun alfahirinta,garkuwan jikinta sannan sanyin idaniyanta Sufyan yazo ya auri hassana wacce ta tare a gydan da sufyan ya kare mata,zaman lafiya alhmdlh nima benaxir omar ina jinjina muku dakukayi hakuri dani duk da matsalan dana rinka samu bansamu na karasa muku da wuriba dakuma rashin cigaba akan lokaci, nagode sosai Allah yabar zumunci Ina gayda rukayya bayero for helping out, yu really made me do dix, Kausar nd ummi aisha na sadaukar da littafinnan agareku don nuna godiyata agareku.

Godiya ga Benaxir Umar da ta rubuta.

Wednesday, 3 August 2016

Hallaccin Sarauta Episode 38

Continuation of Halaccin Sarauta 38

Reqd the previous episode HERE 

Aliya bata iya daga kai ba, tarasa meyake mata dadi, ayayinda falmata da yakolo ke magana, anma falmata tayi kif da ido tareda "cewa tunda ba danki bane saikiyi hakuri" yakolo taji zafin kalman dakinta takoma don abun yafi karfinta, Yusuf nafitowa daga masallaci yaga shehu wanda yayi latti, donsai alokacin zaishiga masalaccin [10/29, 7:10 PM] Adda Bena: Ganin yusuf yasa ya tarbesa tareda cewa

"kayi sauri kashiga ciki kaga ikon Allah hakan yasa yadada sauri jikinshi nabashi wani abu yafaru ne,aikuwa idonsa kan aliya yayi tana zaune a kasa , Allah sarki marainiyar Allah dasauri yaje yadauketa falmata nakiranshi bai kulataba fanninsu yanufa da aliya daki yakaita yaga babu bedshit nan da nan yagane me akayi mata ajiyeta yayi yaje yadauko kettle yahada mata ruwan zafi sannan yace "tashi kishiga," da taimakonsa tashiga bandakin tarufo, jin ta dade baikuma ji motsin ruwa ba yasa yabude bandakin tana zaune acikin bathtub din tana kuka, tausayinsa yakamata bata rai yayi sannan yace "zanmiki wankan" kallonshi tayi adan tsorace anma bai kulata ba, yarufo bayan gidan yakamota, tagara yimasa gaddama, haka yacire kayan yakunna showern kunya duk yarufeta, tagagara motsi haka yacudeta kaman jaririya sannan yadaukota ya ajiye, ya shafa mata mai yaciro mata kaya marar nauyi wani dogon riga ne haka, daya ciro yasamata, yahada mata tea a falo yazo yazauna ya lallabata tasha, itakam sai ganin ikon Allah take, mutumin datake masa kallon soko yau gashi soko na aikinsa,saida ya tabbatar batada matsala sannan yashiga yadau wanka, yafito fannin bayi yanufa, yasa akira masa wanda suka dauki aliya , sannan yafara fada akan me zasu taba mishi matarsa nemo dogarai yayi yasa aka basu jikinsu, saidaya tabbatar kowacce taji jiki sannan yanufi fannin yakolo yagaysheta anan tadada basa hakuri yanuna bakomi , yanufi gun falmata wacce tacika fam tana jiransa, zuwansa tafara masa fada akan me zai hukunta bayi sannan yafara gayda kishiyanta kafin ita, tunda tafara magana baice mata uffan ba harta gama,hakan yakara tunzurata tuni ta kullace aliya aranta, gani takeyi ta mallaka mata da, fitowarsa yanufi gun mahaifinsa suka fara gaysawa, kafin yakoma fanninsa, tare suka wuni har dare alokacin aliya tafarajin wannan kukan kuma, tuni tafara tsorata.

haka suka kara zama adaren basu runtsa ba, tuni aliya tafede rashin bacci yafara takurata. Ga ciwon kai ita saitana jinta asama itabaa kasa ba, baa sama ba, kaman jira kaman ana yawo da ita, Ga rashin kwanciyan hankali haka suka jera sati ahaka bata bacci daredare dasafe kuma inta kwanta saitahau mafarki,ganin abun banayi bane yasa yusuf yakira sufyan suka gayamasa abunda yafaru tunda yake baitaba shiga tashin hankalin ba, nan yafara dana sanin amince mata ta auri yusuf, bai kawo kowa aransa ba anma yasan akwai wanda basuson aliya da yusuf, akwai wani malamin da sufyan yasani donhaka ya umurci yusuf da aliya suje gunshi, Babban malami ne yanada almajirai nan yusuf yabukaci ganinsa, aka musu iso a zaure, malamin yashigo , aliya sanye takeda babban gyale yarufe fuskanta hannunta ne kawai awaje, malamin nazama, yace "subhanallah, ciro abun hannunki" dasauri tafara ciro zobunan, yace "a a.

Na azurfan" cirowa tayi tamika masa, yakarba dasauri ya kira almajiri daya yamika masa sannan yace yaje ya sa awuta, sannan yajuyo yakalli aliya tareda cewa "baiwar Allah kinata yawo da tsafi ajikinki, ai kurwanki ake yawo dashi asama, " tuni jikinta yafara bari, yusuf yakalleta tareda cewa "waya baki zoben?" "Acikin kayan aurena nagani" baice komi ba inda malamin yace sutafi meke tafe dasu, tamishi bayani zalla zallah Yace "dafarko jirin dakikeji wannan zoben ne, shiyake jawo haka yawo ake da kurwanki asama,, nabiyu kuma asiri ne akamaki mai suna janduks, shi wannan sihiri anayine wa mutum inda mutum zaisa ranshi a tsaka," daga yusuf har aliya gyra zama sukayi don kowannensu yagama tsorata jikinsu na bari, musamman aliya, duk dabarun sihiri data karanta bata karanto dawannan ba, "Sihiri ne akewa mutum na kwana ashirin, dafarko akan dauki hoton mutum kowani abu dakika mallaka a yi amfani dashi, sannan wannan sihiri shine zakina jin kukan dabobbin dakikafi tsoro, inkin kwanta kuma zakina mafarkin kura, shiwannan kura zaina binki ne,har kwana ashirin idan kuran ta yakeki zaki mutu acikin kwana ashirin, idan kuma ke kika yaketa zata koma kan wnda yayi sihirin, kinada wani tabo ajikinki dakika samu a mafarkin?" Ta gyada kai tareda cewa "kuran danake mafarkinsa kullum inna tashi sainaga cizon ajikina yayi baki". Yace "haka sihirin take, yanzu zanbaki dabarun karyawa, inbaki karyaba zaki iya rasa ranki Allah ya sauwaka" aliya da yusuf jikinsu na bari sukace to inda yaci gaba da bayani yana cewa "Akofar dakinki ko kuma tsakar gydanki kinemi rami akwai inda aka birne laya kiduba, dole sai an birne laya medauke dasunan wanda akeso ya mutu din,

kinemo acire, sannan inzakiyi bacci kikaranta yasin, fatiha, falaq, nas, da suratul jinni, kikaranta kikwanta zakiyi mafarki anma zakisamu karfin yakanta, donhaka kisamu ki kashe wannan kuran hakan kadai zaisa kizauna lafiya, sannan dalilin ganin wannan kuran wanda yayi asirin kowani dare yana kona laya da takarda me dauke da sunanki donhaka saiki dage da addua wani lokacin mune bama nemawa kanmu tsari, munsan sihiri nakama mutum anma zamu iya karyawa,ki kasance kina bacci da alwala, ki kasance kin rike hisnul muslim,ki guji zama cikin najasa, Allah yana taimakawa wanda ya taimakawa kansa ne" Sunmasa godiya sosai sannan suka mike sukafito dakyar aliya take tafiya jin ance kwana ashirin, acikin kwana ashirin taci bakwai, ashe dama haka abdullahi yaji daya bata kodanta yasan zai iya mutuwa kowani lokaci, ashe haka yaji? Innalilah kuka tafarayi yusuf harya tukata gyda. Sannan yafara lallabinta, dakyar tashanye kukan tafito bilkisu takira tareda cewa tanemo dogarai, suna isowa tafito itama tace sufara tone gun duk inda sukaga laya kowani abu na alajabi su kawo, tana tsaye akansu tana jira nima benaxiratu nadau gatari daya nafara dube dube don naga kozan samu.

To be continue....

Godiya ga Benaxir Umar da ta rubuta.

Saturday, 30 July 2016

Hallaccin Sarauta Episode 37

Continuation of Hallaccin Sarauta Episode 37

Read the previous episodes HERE

falmata kashe kanta ne batayiba domin amincewar da sarki yayi, ta tura duk wanda take ganin zai iya magana wa sarki anma taci tura, waliyyim aliya shine alh.hussieni anma sufyan yayi kif da ido akan bai san zance ba, dole akarshe aka bukaci alh.hamidu yazama waliyyi, duk soyayyan dayakewa hassana yayine domin yasamu hankakinta anma daga karshe yaga sone na gaskiya , hussiena ma tasha alwashin zaman lafiya kam aliya da yusuf bazasu sameshiba agydan Anyi zama a kotu inda lawyernsu sufyan yaci karan, kotu tabawa alh.hussieni zaman prison na shekara ashirin da daya sannan ta bukaci daya fidda gadonsu ko kuma kotu taci tararsa, a ranan aliya tayi kukan farim ciki tunda take bata tabajin kwanciyan hankali irinna ranan ba, jitayi kaman ansauke mata dutsen badr akirjinta, tuni ta maida hankalinta kan batun aurenta duk da tasan tashin hankalin dazata shiga, antyn abuja ne ta bukaci taje don su samu ayi siyayyanta, ta tattara dan komatsanta duk da yusuf bai so ba, shi yanzu babban damuwansa yaga ya aureta, Sunyi sallama tatafi yayinda yakoma fada, shigansa yatarar da bilkisu da abincinsa, zama yayi yarike kai yana tunani kansa yamasa nauyi har yanzu falmata taki yarda da auren, yasan son zuciyanta ne anata tunanin wai saidai ya auri hussiena, shi haryau hussiena bata kwanta masa arai ba , bilkisu ce tayi tari hakan yadawo dashi daga tunaninsa yakalleta sannan yace "meke faruwa acikin gyda gameda aurena" kanta a kasa tace "Gimbiya yakolo tafara shiri, yayinda gimbiya falmata bata fara ba, ita shirinta da hussiena takeyi" Baice komi ba yatashi yafice sannan yanufi fannin falmata anma sa iso sannan yashiga daga ciki tana zaune akan kujera yazauna akasa abinda bayayi, hakan yatabbatar mata da bukata yazo dashi, bata kulashiba yasa kanshi akasa sannan yace "Ina neman amincewarki na auren aliya" "Ban bayarba, kuma ko bayan raina ban sa baki ba" "Inaso kibani hujjanki wanda addini ta haramta min auren aliya" "Yar kan titi!! Yarinya tagama gantalinta agari! Kowani dan iska ya kwasa! Kainan tayi fitsari tabaka kasha ba dole kabiya kaman agwagwa ba!" Ga mamakinta taga yamike yafice , baikuma cewa komiba, tunda shi mahaifinsa yasa albarka hujjanta ba kwakkwara bane dazatace masa kar ya auri aliya, fannin yakolo yaje, yasami hauwa tana ganinsa tafice don haryanzu tsoronsa takeji, yakolo tayi murmushi tareda masa iso, bayan karasowarsa yazauna dum a kasa, nan da nan tagano alfarma yazo nema, yagaysheta ta amsa masa sannan yace "Naje gun gimbiya na nemi ta amince min auren aliya taki yarda, kuma hujjojinta ba ingantattu bane, kitaimaka ko zakisa baki" "Bakomi yusuf, kasan mahaifinka inta sa rai akan abu, kai yakamata ka lallabata anma zan gwada kokarina kaji"

"Nagodr Allah yasaka da alheri" Ficewa tayi, tuni abdullahinta ya fado mata arai, tasan yarinyar dayakeso aketa rikici akai, gashi cikin mata yafara fitowa duk da sunriketa tana fadan akan saita haihu tukun zasu barta tafita, Yakolo tayi iya kokarinta don fahimtar da falmata anma falmata kaman ana zuba mata man fetur, dahaka biki ya matso kusa aliya tadawo gari saidai tagagara zama, rokon yusuf tayi akan ko zai taimaka yabata aron bilkisu, haka kuwa akayi , tuni bilki tafara taimaka mata, jin aliya zata auri dan sarki tuni dangin nesa da wanda aka manta dasu suka fara bayyana kowa saiyace yazo auren marainiyan Allah, Ran jumaa aka daura auren aliya da yusuf, inda akayi dinner daredare nagani nafada, munsha gwaggori munsha rawa,yusuf na makale da matarsa, hannunsa gam anata shi yanzu gani yake duk duniya bawanda yakaishi hakuri da juriyan dayayi, angama dinner inda aka kai amarya fanninta side guda aka ware mata a fada, dakuna uku da falo biyu,tabbas tasamu kaya tasha gata, sufyan yashare mata hawaye tayi kukan rashin iyaye anma batayi maraici ba, kowa yayi mamakin ganin yadda falmata tasake ranta da maganan biki, harwani jan aliya take ajiki, acewarta komi yawuce,anma aliya tagagara sakewa da ita, randa aka kaita an watse aliya tana kunshe jikin gyalen kyabban da aka rufata dashi duk ta kagu tana jiran angon nata,don tsoro takeji dakin ya mata girma sosai, kukan kare tafaraji, dafarko bai dametaba anma datayi tunanin gydan babu inda aka ajiye kare, tuni tafara tsorata kodai yusuf yasiya ya ajiye a fanninta ne? Toh anma matsalanta shine jin kukan take kaman agabanta yakeyi, hannunta ne yafara bari tafara salati da dan karfi sannan taji shiru, can kuma takarajin kukan karen daga nesa saikuma karan kofa, saura kadan tasake fitsari awandonta taji anbude kofan, yusuf ne batasan lokacin data rungumoshiba, jikinta na bari jinhaka yasa shima ya kamata, sunfi mintoti ahaka kafin yajawota yazaunar da ita akan lallausan gadon,

"leeya meya sameki?" Bata bashi amsaba, tafarajin wani kukan karen wannan karon harda kulya, salati takeyi jikinta na bari, tuni jikinsa yayi sanyi domin bata cikin hayyacinta, alwala yadauro yace itama tayi anma dole saida yarakata toilet din don tsoron datakeji. Tafito yajasu sallah yakamo kanta yatofa mata addua, sannan yafara tambayanta akan littafai daga kan fiqhu, hadiths da dan tauhid, yayi mamaki sosai dayaga tanada sani, baitaba zaton tasani sosaiba, daganan ne yace "mezakici?" "Babu kabarshi" Cire mata kallabin yayi, sannan yarikota naman ya yaga kadan yafara bata tana tauna ahankali yabata da soya milk haka taci takoshi sannan yace tadan kwanta, tana kwanciya taji kukan karen zumbur tamike kaman an tsira mata allura, rikota yayi yana tofa mata addua, atakaice haka suka kwana a zaune har asuba, dazaran zata kwanta sai kukan kare ko qulya, asuba nayi sukaji shiru, hakan yabashi daman fita masallaci, tana sallah bata fitoba saboda baccin daya kwasheta, karfe shida daidai saiga umma uwar tsoro falmata ta turota buga mata kofan tayi can dai tabude, bata tasheta ba ta nufi kan gadon taja bedshit din tafice, kaiwa falmata tayi wanda tana zaune tana jira ganin babu komi akan bedshit din yasa ta salati, tana cewa "saida na gayawa yusuf wannan yarinyan tagama gantalinta, yaki yarda, kue kudauko min ita," Dauko aliya cak akayi aka wurgata akasa. Jiri ne yake dibanta anma tuni ta warsake don ruwan sanyi tas falmata tasa aka watsa mata, alokacin yakolo tazo ranta yayi mummunan baci, inba raina darajan dan adam ba yazaayi matar danki dan cikinki zakina wulakantawa? Tuni fa gyda ya hargitse, nima benaxiratu idona na rufewa anma dole nabudesu don ganin mexai faru.

To be continue....

Godiya ga Benaxir Umar da ta rubuta.

Saturday, 23 July 2016

Hallaccin Sarauta Episode 36

Halaccin Sqrauta Episode 36

Read Previous Episode HERE

jakadiya tana rusune harta mike ta fice. Bawanda yakai falmata farin ciki aranan saboda tana ganin wanda zai tare mata sarautar danta yafadi kasa yamutu, shehu kuwa baiyi hankalin dazata sashi a sahun masu karban sarautan ba. Donhaka tuni tafara tunanin hanyan dashi kanshi sarkin zai mutu, babu tsoron Allah babu tunanin lahira, tunaninta shine takashe duk wanda tasan zaishiga tsakaninta da mulkin garin, Sai dare sannan aliya tafarka atake sufyan ya tallabota yadawo da ita gida yana ganin inna baikulataba yashige da aliya ciki, saida yatabbatar takwanta ya rufo kofan sannan yafito inna tana tsaye tana jira yafito, baikulata ba tana kiransa, inba don babu gun da zaikai aliya ba da gidan nata saisu tattara subar mata shi, Cikin dare aliya tayita firgit tana wasu mafarkai, dolenta tamike,alwala tadauro tafara sallah har asuba tana yiwa abdullahi addua, tausayin matanshi da abunda zasu haifa yacikata, Dasafe sufyan nazaune wayansa tayi kara alh.hamidu ne yake cemasa yazo suna jiransa, baiyi bacciba tsabar yana tunanin hanyan dazsi bullowa maganan, motansa yaja yafice gydan alh.hamidu yanufa suna zaune a tsakar gydan suna jiranshi, sun gaysa yabasu girmansu sannan yazauna, inda hussieni yake tambayansa alkawarinsa, sufyan yayi murmushi sannan yace "komi zaizama naka idan kabani tarihin yadda akayi ka kashe mahaifina!" Ba hussieni ba har alh.hamidu saida yabude baki don mamaki,hussieni yagagara cewa komi,hakan yakara tunzura sufyan, hawaye ne suka fara zubo mishi yafara magana cikin sanyin jiki "Ashe karshen duniya zatazo dahar danuwa zaisa hannu yakashe danuwansa saboda dukiya?saboda mulki?" Bawanda ya amsa mishi kaman tsoffin barayi da aka kamasu hussieni kanshi akasa yafara magana "kai mahaifinka ne.

Nikuma danuwana , wlh tlh ba abunda nashirya yafaru ba kenan, Allah dai yayi zanzama sanadi, tabbas munyi musu da shi batun mulki anma ban kwallafa raina ba. Nasan na umurta da amai dukka anma bance sukasheshi ba, bankuma ce suhada da mahaifiyarka ba. Allah yayine lokaci yayi don Allah kayi hakuri, karkuma kabari kanwarka taji alokacin sufyan yayi kukan zuci daya tuna da iyayensa anma tuni ya watsake saboda ayanzu zucuyarsa tabushe yana tunanun daukar fansa, recordern dayake recordn yasawa stop sannan yamike yafice batare da ya ce musu komi ba dama yakira lawyernsa awaya tuni yadamka masa shaidansa tareda basa go ahead nashigar da kara kotu, koba komi yanzu yaji sanyi aransa

Aliya kuwa tacanja gabadaya ba abinci sai ruwan lipton, sufyan yayi lallamin harya gaji yusuf ma yayi nass Bayan sati biyu alokacin anwatse a gun rasuwa. Sannan alh.hamidu da alh.hussieni sun shiga kotu inda zaa fara sauraren karansu Aliya tadan sake, yanzu hankalinta ya kwanta maganan rama mutuwan iyayenta anmma abunda yafi bata ciwo shine danuwan mahaifinta shi yakashe mahaifinta. Abunda ciwo,saidai yanzu tabar komi agun Allah har lokacin sufyan baya magana da inna , aliya tayi iya kokarinta anma yafaskara yusuf na iya kokarinsa ganin ya farantawa aliya yayinda soyayya mai karfi tashiga tsakaninsu, tuni yafara maganan aurenta yasamu falmata da zance atake tace batasan zance ba, nan yakoma kan yakolo ta yadda takuma sa albarka inda anan yasako waziri da sarki, dafarko waziri yaki amincewa acewarsa dole yusuf yadauko yarinya mai asali, nan fa yusuf yazayyana masa rayuwar aliya tundaga farko dakuma wahalhalun datasha waziri yayi mamaki sarai anma yace zai gwada tunkarar sarki, sarki yanajin magana yatambayi wacece atake waxiri yace yar marigayi galadima,sarki yaji dadi sosai tuni yafara murna, wannan yarinyan ai ita keda asali, nan waziri yace "anma akwai matsala mai martaba, yarinyan tashin hannun mace tayi dakuma tashin gari" Sarkin yayi shiru don tantance me wazirin ke nufi donhaka yace "yi bincike mai tsanani muji"dahaka waziri yabar maganan, falmata taji labarin abunda ke faruwa donhaka ta nufi sarki da maganan anma yanuna mata shi ba ruwansa,don

shikanshi yanaso yusuf yayi aure, baitaba tsammani kuma yusuf zaikawo yarinya yace yanaso ba donhaka tuni tarikice duk tana tunanin hanyoyin dazata hanashi wanda shi yusuf har daina zuwa gaysheta yayi tsabar yasan kalan mitanta, Aliya kuwa tasan bakaramin rikici bane zai afku donhaka tuni tafara lura da takunta, ga masu nufinta da sharri, ita anata taso ta tattara tabar garin bata da dsmuwa da gun anma dole tajira a idar da case din iyayenta a kotu, Waziri yayi iya bincikenansa akan aliya tuni yakira yusuf "Kana sane da tayi bauta agydannan?" "Tayine alokacin batasan kowa ba" "Kasan dai yanayin rayuwarta bai shiga danaka ba" "Nasani shiyasa nake rokonka daka sa baki, kaikadai ne inka yabeta sarki zsi yadda, don Allah kataimaka" "Zan yi iya kokarina, anma kai kasan halin mahaifiyarka" Dawannan suka rabu inda yaje yagabatar da zancen da duk wani tarihin aliya agaban sarki, sarki yadannan approve makake, nima dai benaxir na dannan approve duk da munsan amincewan mezai jawo, ansa rayuwar aliya cikin hatsari da damuwa, anma munsan cewa aliya ce kadai zata iya gyrawa falmata duwawun zama, muje zuwa gobe insha Allah saina dora.

To be continue....

Godiya ga Benaxir Umar da ta rubuta.

Wednesday, 20 July 2016

Hallaccin Sarauta Episode 35

Read the previous Episode Here

Mota ya fizga dakarfi sai alokacin aliya taga jikinta ajike anan ta tabbatar da aefa fitsari tayi anma wayake tanan yanzu, tunda kayan jikinta ba nunawa zaiyi ba goran ruwa tagani a motan tabude ta watsa ajikinta, fada yanufa dasu suka sami gurin acike, dakayar yasamu gun parking yana tafiya aliya tabi sahunshi fannin yakolo suka nufa wacce babu matsaka sinke ancika, tundaganan jikin aliya yayi sanyi komawa tayi tazauna, agefe wasu hawaye masu zafi suka fara bin kumatunta sufyan ne yakamo hannuta suka shiga shima dataimakon hauwau. Wacce tanuna cewa su yan gida ne suna shiga dakin acike agefe aliya ta tsaya sufyan yakarasa gun, abdullhi ne akwance agun macecce, duniya inazakije damu, mun aikata alheri mun mutu munbarta, dole kowani rai mamace ne, sufyan durkusawa yayi agun tuni dogarai sukayi gefe dashi don baabarin kowa kusa da gawan. Yakolo ma ba kanta dakyar aka danneta, aliya kuwa wani kyalli kyallu take gani a idonta tuni ta fizge dankwalin kanta tajuya dagudu zata nufi kan gawan rikota akayi, tuni sufyan shima yamike yarikota yusuf wanda ke can kuryan daki tuni

yafito ganin aliya tuni ya nufa kanta rikota akayi anma yadda kukasan karfin aljannu gareta wani fizga datayi bashiri suka fada tabaya kan abdullahi tanufa zata budeshi anma nanma dogarai suka kara rikota, tuni umma uwar soro tace a fice da ita, daukanta cak akayi akafice da ita, wani irin kuka takeyi wanda duk mai kallonta sai ya tausaya mata, itakanta tadawo abun tausayi , sumbatu takeyi "yarima meyasa zakamin haka? Yarima meyasa zaka tafi baka amsamin tambayoyin dake raina ba? Kasan cewa sanadina kamutu anma baka gayamin hujjanka ba! Innalilahi wainna ilaihi rajiun!" Kuka takara fashewa da, yusuf ne yajata, yasa aka nemo bilkisu tarikota suka koma gefe acewarsa akaita fanninshi harsaitayi shiru kafin tashigo cikin jamaa, Anyiwa abdullahi wanka yadda ake kowani mamaci, abdullahi kuwa yasha fatan alheri agun alumma, iyayensa sun sakamishi sunkuma nema mishi aljanna, hatta mtanem gydan dsuke karkashinsa suna aiki kowa alheri yake fada akan abdullahi, duk wanda yazauna da abdullahi yasan mutum ne mai tausayi, marar son fada, mai son gaskiya, mai adalci mai kuma bin hakkin dan adam, matarsa da mahaifiyarsa sunbada kyawawan shaidu suma akansu, a inda sarki dakanshi yake jawabi amfanin zuwa duniya kenan, kazamto nai kyautatawa mutane , kazamto

mai tausayi karkace don kafi karfin wane, ko wane yana aiki akasanka ka wulakantashi , kasani cewa shaidun duniya shine shaidan lahiranka, muguji duniya muzamto masu shiri akowani lokaci don ziyartar kabari, musani cewa aikin damukayi duk yana cikin littafanmu, yakuma yi jawabin cewa kar mutane suce don abdullahi yabada kidney dinshi shiyasa yamutu, wannan bahaka bane lokacinsa yayi, daya bada da bai bayarba dukka Allah yayi zaimutu yau, kuma mutane susani cewa akullum idan aka tambayi abdullahi maganan kidney dinshi da dalilin bayarwa yanada hujjojinsa anma babbar hujjarsa itace yayi alkawari kuma a matsayinshi na dan musulmi, na wanda yataso cikin mutunci da daraja a matsayinsa na balagagge wanda yasan hukuncin marar cika alkawari hakan yasa yacika alkawarin, kuma shi sarki yana alfahari dashi hakkika abdullahi abun koyi ne, Allah ya sa mucika da imani Ansamu ankaishi makabarta kafin sudawo aliya tasuma yakai sau uku, haka kawai takejin haushin kanta gani takeyi kaman itace musabbabin dalilin dayasa abdullahi yarasu, dakyar aka mata alluran bacci tasamu ta kwanta Sufyan kuwa abun duniya tamasa yawa dawanne zaiji, mutuwan amininsa kokuma bincikowan dayayi cewa hussieni shiya kashe mahaifinsa da mahaifiyarsa, dawani ido zai kalleshi duk yaga missed call dinsu anma bai dauki ko daya ba, atunaninsa basuda abin fada mashi gun inna yanufa yatarar tana kan sallaya tana ganinshi tashafa addua tareda cewa "sufyan ya akaji da hakuri?" "Alhmdlh" "Allah yajikanshi yamishi rahama" "Amin inna, dama nazo muyi maganane akan alh.hussieni" "Inajinka" "Kinsan shiya kashe iyayena shiyasa kika boyemin ko?" "Hmnm abdullahi kenan, rasuwa fa aka maka yakamata kayi hakuri ai yanzu ko" "Yanzu nakeson kifadamin amsata" "Nasani. Sannan alh.hamidu ma yasani, munga babu amfanin gayamuku ne,kuma nagayamaka anan nagayamaka, sufyan kadaina bincike, addininmu ma batason irin wannan binciken, tasar da kwantaccen magana,ana zaman lafiya kunje kun binciko abunda zai hanaku zaman lfy, yanzu dakasan cewa shine mezakayi?" "Lallai inna kinban mamaki, tambaya kikayi mezanyi? Kotu zamu shiga!, bazan hakura ba harsai anyiwa iyayena adalci, kina nufin

muna ji muna gani ankashe iyayenmu a banza kenan? Da ke! Da duk wani wanda yakeda hannu aciki wanda yasani da komi duk sainakaiku kotu, zaku fuskanci hukunci " Baikulataba yafice duk da ta tsorata tana kokarin yimasa bayani, fada yakoma har lokacin ance aliya bata tashiba ganin yusuf yayi donhaka yaje shima yazauna agefensa, yusuf na zubarda hawaye yace "kasan dalilin da yabata kodan shi?" "Nasani" "Menene" "Don yamata alkawari zai kareta koda ranshi zai cire yabata" "Bayan haka" "Yana sonta!! Itace mace tafarko daya fara so a duniya" Yusuf dama yasan dahakan yana son ya tabbatar dinne, ajiyan zuciya yayi wanda shi sufyan yagagara ganewa ko na farinciki ne ko na bakinciki Acan cikin fada kuwa fannin falmata jakadiya ce tashigo tana murmushi, falmata ta kalleta itama murmushin take, jakadiya tafada kasa tana kirari Sai ke Jaruma a cikin jarumai, jaruma acikin jagororin ma jagoranta Idan akaji ance kasaita in anduba kin cancanta taimako dare zuwa rana kin sabayi wa al'umma mai dukiya mai ran karfe Mai kudi uban matsiyata baki fushi ko anzage ki Baki zagi ko anzageki ja muje kece gimbiyar magimbiyata kara masu kece babbar su Mai girma agidan girma sannan kuma matar mai girma,uwar gida a gidan mai girma,Mai hidima a gidan hidima sannan kuma matar mai hidima, farin cikin mai hidima, zuciya hasken annurin mai hidima, zakanya saidai aganki anesa badai a matso kusa ba," Wani irin murmushi da dariya falmata tayi cikin jin dadi, ta daga giranta sama sannan tace "kinga na kashe da' saura uwarsa sannan uban gayyan uban gidan, yusuf shine sarki ba waniba"

To be continue....

Godiya ga Benaxir Umar da ta rubuta.

Monday, 18 July 2016

Halaccin Sarauta Episode 34

Halaccin Sarauta Episode 34

Read the previous Episodes HERE

tuni suka fara tunanin hanyar dazasu je su sameshi ko shi yazo, Washegari sufyan yaje gun alh.hamid tareda rokonsa ko akwai hanyar dazaayi asamu hussieni yazo, yace mishi hanya daya ne kadai zaisa hussieni yazo, in ance mishi anga ajiyan mahaifinsa, ajiya ne wanda kakanku yayi wa hussieni haryau baasamu ba, donhaka dole kusamo wannan hajiyan don hussieni yazo, sufyan ya amsa da toh anma shi tuni ya shuka dabararsa, wasikar jaki yayi yasa aka tura inda yake fadawa hussienin shine dan hassan kuma ga ajiyarsa a hannunsa, yayi hakkanne don baida kudin dazaice zaije bayan haka baisan yadda kanin mahaifin nasa zai karbe sa ba, gwara yajawo shi yazoshi duk da taimakon alh.hamdiu yanemi address din yatura Aliya ta warke garau haka ma abdullahi rayuwa tacigaba da gudana musu, duk da aliya ta dan ja baya da yusuf anma tana sonsa , daidai da kankanin lokaci sonsa baitaba raguwa mata ba, abdullahi kuwa yanzu da taimakon injin bature yake rayuwa, yariga daya cire rai wa duniya don yasan wahalarshi tazo karshe.

Acikin wata biyu wata rana sai labari ta iso sufyan cewa ga hussieni yazo gari, ya tare ne agydan alh.hamidu hakan yasa aliya da sufyan suka shirya tareda inna don zuwa gayda shi, kasancewar sunsaba da gydan shigansu sunyi mamaki don kammanin mahaifinsu ne sak a fuskan hussieni sai yanmata guda biyu wanda duk daga kallonsu ansan yan biyune, zasuyi saan aliya, kyawawa dasu suma kammanin mahaifin suka dauko, hussieni ya tarbesu sosai a matsayin yayansa, aliya taji dadi ganin cewa itama gata da yanuwa tuni suka saba da yanbiyun, sunsha tadi sosai sai can dare sannan su aliya suka dawo gyda Washegari sufyan ne ya koma anma wannan karon duk acikin gyda suke, alh.hamidu da hussieni suna falo donhaka sufyan yashirya don yaje yatambayeshi yarike hannun kofan zaishiga yakasa kunne donjin mesuke fada, Alh.hamidu yace

"kasan cewa yarannan sundameni maganan mahaifinsu sai tsananta bincike suke, ni bansan mezance musuba, kasan dai bazan bude baki nace musu hussienin mahaifinsu shiyasa akashe mahaifinsu don samun sarauta" "Nagode daka rufe maganan baka furta ba, ni bansan tayaya zanyiba, nayi nadaman abunda na aikata gashi idan ina kallon yaransa duk sai naji na tsargu mussaman macen, itace na cuta da maraici, hakika son zuciya da zugin shaidan su suka sani na aikata abunda nayi,yanzu kunsamamin ajiyan ne? Don da wannan ajiyan zan iya karban sarautar sarki bana galadima kawai ba, nadawo gida bazan koma ba,"

Sufyan dake rike da hannun kofan yasake jiki a sanyaye yafice batareda kowa yasaniba, gyda gun aliya yanufa yashiga tana bacci don tace mai haka kawai takejin faduwar gaba da ciwon kai yace tayi bacci inta tashi tasameshi agydan alh.hamidu, zura mata ido yayi hannunsa na bari yana shafa gefen fuskanta, farkawa tayi tazauna tareda cewa "yayah" bai amsataba yafara kokarin share hawayensa, tunda take bata taba ganinshi awannan yanayun ba, tuni jikinta itama yahau bari "yayah! Meya faru? Waye ba lafiya?" Hannunsa na bari yariko nata yarungumota kuka yake sosai mai tsananta zuciya, tuni tafara itama duk da batasan dalili ba, cikin yanayin tausayi yace "aliya hakika agarin bincikenmu yau mun bincikawa kanmu tashin hankali, aliya alh.hussieni shiya sa aka kashe mahaifinmu" tsak ta tsaya tana kokarin daidaita numfashinta anan wayan sufyan tayi kara cikin yanayin tausayi yadauki wayan, "hello, naam" Salati taji yafarayi yamike cak "abdullahi? Innalilahi!! Innalilahi wainnailaihirajiun!! Gamunan zuwa! Innalilahi!" Fitsari tasake awando wani kuka yaci fuskanta, gabanta ya tsananta fadi, "yayah meya sameshi?" Baikulata ba yace "shirya mutafi" dankwali kawai tadauka tabishi, nima benaxir gabana yana fadi nabishi don ganin meya faru!

To be continue....

Godiya ga Benaxir Umar da ta rubuta.

Wednesday, 13 July 2016

Halaccin Sarauta episode 33

Continuation of Halaccin Sarauta episode 33

Read the previous episodes HERE

Jawowan dayayi yaga bangon envelope ne donhaka sai ya ajiye agefen pillow, yana zaune har yusuf yazo mikewa yayi yafice don tun randa yusuf yaje yacemar yagode baikara mishi magana ba. Har abdullahi zaifita yusuf yace "tsohonka na memanka" gabanshi ne yafadi dum donyasan ba maganan dazaamishi saina maganar bayar da kisney dayayi shiyanzu matarsa yake jin tausayi karya mutu su gaza kulawa da ita da dan cikinta, dakin yanufa yatatara abunda zai dauka yafice gyda yanufa yayi wankarsa matarsa duk ta tsorats don tasan baa sallameshiba yadawo, ta so tabashi abun karyawa baikulata ba yafice don ganin sarki mai ran karfe baisameshi ba don yana bacci dole yahakura yakoma Yusuf kuwa zama yayi dirshan agefenta ya tsura mata ido.

Tadawo gangar jikinsa tadawo wani gurbi arayuwansa itace tsoka da jininsa, tadawo tamkar bugun zuciyanta domin duk numfashin datayi sai yaji kaman daga jikinsa ne, bata farkaba sai takwas na safe likitan yaga warkewanta dawuri yakuma ce taci abinci sosai wanda ada ruwan lipton suke bata da abu mai ruwa hankalin kowa ya fara kwanciya banda na aliya damuwanta su sallameta awannan asibitin don tasamu tafita ta cimma burinta, sufyan ne yashigo alokacin yusuf yashiga gari anan ta mai bayani sannan tabada takardun daya karanta shima ya yarda da magananta nacewa saita gun alh.hamidu, donhaka yace zai danne damtse don yasamu kusanci da mahaifin hassana, alokacin kuma ta tambayeshi ko yasan dalilin dayasa abdullahi yabata wani bangare ajikinsa, bayaso yatada mata hankali donhaka yace "kinsan abokina ne, amintan dake tsakaninmu yabi," bata gamsu da bayaninshi dama yasan bazata yarda ba, zatamai wani tambayan ya tallafota tare da cewa ta kwanta tayi bacci, hakan yakara tabbatar mata akwai dalili yusuf ne zaigayamata, saidai tatuna guntun kishin shi donhaka ta share, tuni ta gargade zuciyanta da kartayi binciken dalili balle yadawo mata tashin hankali,

Dagari yama wayewa abdullahi yakoma gun sarki inda a tunaninsa fada zaimasa. Yamasa fadan kuwa sosai tareda cewa inhar kanaso ka gwada hallacinka kamata yayi kasiya, yanzu kai zaka iya mutuwa duk lokacin da jikinka ta gaji da wannan injin, nan dai abdullah yasha fada anma daidai da second daya baitaba nadamar abunda yayi ba, Satin aliya daya aka sallameta tuni takoma gida ankara gyra fanninta tasan aikin sufyan ne da antyn abuja wacce aranar tawuce abj, duk da tadawo gida mutane basu dauke kafa ba. Don gaydata alokacin sufyan yasami kusanci da nahaifin hassana tuni yashirya randa zaimasa tambayoyin hotunan yadiba sannan yaje gydan, hassana ta tarbeshi sannan tamasa iso bayan sun gaysa sai sufyan yayi bayanin meya kawosa tareda hotunan ya ajiye mai,alh.

Hamidu yayi murmushi sannan yace "dama nakai shekara sha biyu inajiran rana irin ta yau, ranan da yayan cikinsa zasuxo don jin bayani saidai nasan ku biyune, ina kanwarka? Kaje kadaukota itama tanada hakkin tasan meyasami mahaifinta" sufyan yace toh tareda ficewa gyda yaje ya kinkimo aliya a mota yamata bayani tuni jikinta yayi sanyi domun ta tsorata sosai, suka koma inda suka sameshi kamar yadda sufyan yabarshi yafara dacewa "iyayenku yan biyu ne masu son juna dakuma matukar kama, hakan yasa shakuwa a tsakaninsa, sarauta da son mulki shiya shiga ransubwanda shaidan yazo yashiga tsakani , bazan taba fada muku waya kashe iyayenku ba saidai ina rokonku dakuyi hakuri, ku yafewa kowaye ne, ku manta, don tsananta bincike baya jawo komi sai bacin rai," sufyan da aliya duk sun kagu suji bayani anma sai waazi yake akarshe yace "ranar karshe da mahaifinku da hussieni suka gana adaki kafin hussieni yabar gari, bawanda yake gun sai ni danake falo suna daki abunda naji kuwa shine hussieni yace ko duniya zata juya saiya mulka garrinnan, yayinda hassan ya musanta , hussieni kuwa yace su zuba sugani" donhaka kuhakura da binciken haka" sufyan da aliya sunyi sunyi anma mutum kam ya gunshe baki a bacin rai suka fito suka fice, hassana wacce tashirya don soyewa da masoyinta sai karar mota taji yafice, .gyda suka isa inda akarshe suka yanke shawarar dole mutum dayane yazama ansansu, hussienin mahaifinsu!

To be continue....

Godiya ga Benaxir Umar da ta rubuta.

Tuesday, 5 July 2016

Halaccin Sarauta episode 32

Continuation of Halaccin Sarauta episode 32

To read the previous episodes click HERE

Fita sukayi adakin suka barta da bugun zuciya har cikin ranta ta tsorata kwanyanta yafara caji, tasan haka kawai mutum bazai cire koda yabayar ba, wani zuciyan tace yanzu haka tsabar zumuncin dake tsakaninku ne, harta bar maganan ahaka saikuma ta tsorata data kara tunawa sunce guda dayan data rage masa yabayar, inna ce tariketa ta kwantar da ita anma aliya ta gagara kwanciya duk ta tsure hankalinta yatashi tuni tamike a tsaye tana cewa "inna nikam ko dai zanfita ne? Ina yaya?" Duk a gigice take hakan yasa inna tarikota tareda cewa "kwanta, barin kira miki yayankin" fita tayi don tanemo sufyan bata ganshi ba donhaka saitayi magana da nurse daya don su samu sudubata a lokacin shigowansu jikin ya rikice aliya duk ta tsorata sosai nurse dinne ta rikota itakuwa duk ta gigice dakyar aka kwantar da ita wani irin kuka take mai shiga zuciya tana kama jikin inna,

"inna kitaimaka kinemomin yayana" batasan meye matsalarta na, anma ta tsorata bashiri tafita duk da batada tabbacin ko zataga sufyan din filin asibitin tanufa tazaga bataganshiba donhaka takoma ta dakin abdullahi tanufa ganinshi azaune a rikice tace "yarima ina sufyan? Kataimaka ka nemoshi munshiga uku aliya" agigice yamike yacire kalulan hannunsa sannan yace "muje" dagudu gudu suka nufi dakin alokacin aliya ta bankade nurse din tana cewa akaita gun sufyan, abdullahi ne yakomota yariko hannunta sannan yace "aliya kikalleni" kallonsa tayi agigice tarude anma yadda ya zura mata ido tuni taji wani nutsuwa yashigo mata, ya kwanto mata, hannunta na bari tace "yariiiiiim" "Shhhhh karkiyi magana kiyi shiru" Shirun tayi kaman yadda yace addua yatofa mata sannan yace wa inna insha Allah bazata kara firgita ba, zama yayi dirsham agefenta acewarsa sai sufyan yazo zaitafi, wata nurse ce tashigo tareda rokonsa yakoma daure fuska yayi kaman yaga malaikar mutuwa yana cewa ba inda zanje kuma karta nima takurashi, hakan yasata fita don tasanar da manyanta, inna tayi tayi dashi yamike yafice anma yaki yarda, tuni tafara nadamar kiransa anma abdullahi yakafe, aliya kuwa tana jingine a kwance tana ta tunani, tarasa tayaya zata tambayeshi inkuma yabata da zuciya daya ne fa? Yazatayi? Wani irin nauyinsa takeji yanzu fa duk gadaranta akwai kidney dinshi ajikinta, ita damuwanta sufyan yazo ta tambayeshi gaskiyan alamarin, Sunfi minti talatin ahaka kafin yashigo, shigowarsa yasamu aliya tayi bacci abdullahi na gefenta, tuni yanufo kansa, "kaida bakada lafiya kazo gadin wata marar lafiyan?"

"Kai nake jira kadawo, firgita takeyi shiyasa nayi hakan" sufyan ne yajashi suka nufi dakin da aka kwantar dashi, sannan yadawo dakin da aka kwantar da aliya sannan yazauna cikin mintuna kadan saiga bilkisu dama sufyan yaroka abarta tafito don sunfi sabawa da aliyan yakolo ta amince, shigowan bilkisu dole tajira aliya ta tashi bayan farkwanta alokacin sufyan yanufi gun abdullahi , aliya naganin bilki ta wangale baki sanin cewa zuwanta bana banza bane bayan bilki tamata jajen yajikin sannan tamika mata wani takarda tare da cewa duk abunda kikeson sani yana cikin nan, Allah yabaki saa, bashiri tafice don tsoro takeji Aliya ta paki idon inna tasaka tacikin bargo taboye sannan takoma ta kwanta, can dai tamike tasaka akasan katifan tamayar ta kwanta.

Bayan sun watse daredare anbarta da inna wacce tabude baki sai bacci take, taciro takardun tabude hotuna ne tsoffi dakuma wani enlarger karami, mahaifinta ne da alh.hamidu mahaifinsu yan biyu saikuma sauran biyun su uku, da mahaifinta dawani wanda take kyautata zaton cewa shine dan biyun mahaifinta hussieni sai alh.hamidu gabanta ne ya tsananta fadi, ta mugun tsorata asaninta tace bilki ta bincika mata alakan alh.hamidu da fadan gidan kusancinsu ta bakin tsoffin bayin dasuka san kan gydan, karshe kuma ga abunda bilki takawo mata, tasan bilki batayi makaranta ko ilmin dazatayi wannan binciken ba, dole akwai wanda yasan sirrinta, waye toh? Sufyan? Inhar shine toh bazai bawa bilki ba dakanshi zaiboye. Abdullahi? Tasan abdullahi bazai taba kawo aikinta ba, don baigama sanin alakarta da sufyan ba balle abunda yakawota(a tunaninta abdullhi baisan cewa ita kanwar sufyan bane), yusuf? Salati tayi tabbas yusuf ne shine kadai namijin da yasan sirrinta , amma meyasa yataimaketa? Nanma dai tagodewa Allah damuwanta burinta yakusan cika, yanzu dole tasami hanya da alh.hamidu don taji daga bakinshi meya sani, tunda duk shine mafi kusa acikinsu Batayi bacci ba har asuba nurses sunzo sun dubata suka fice ana idar da asuba bacci ya kwasheta, abdullahi ne yashigo dakin don ganinta inna tana wuridi yadan zauna agefe, idonsa ce tahango mai takarda, jaa yayi don yaga menene (Salam, akwai batu jiya dayayi ta zagawa akan na rasu, ba ni bace wata benazir muhd ce yar nasarrawa, nagode ga dumbin masoyana dasuka kira donjin lafiyata, duk wanda aka tayar ma hankali ko yashiga wani damuwa ina rokon afuwa don Allah nidai ina raye, Allah yabamu tsawon kwana,)

To be continue....

Godiya ga Benaxir Umar da ta rubuta.

Saturday, 2 July 2016

Halaccin Sarauta episode 31

Continuation of Halaccin Sarauta episode 31

To read the previous episodes click HERE


Bai amsa tambayanta ba yace "yajikin naki? karki kara magana" bata kara cewa komi ba, tana tunani ne taga waye yabata, taga yusuf garau donhaka tasan bashi bane, sufyan ma taganshi tasan bashi bane, taga inna taga antyn abuja duk sauran tsofi ne donhaka taciresu a lissafi, saikawai tasa aranta na siyarwa aka saka mata, nan tafara adduan Allah yasaka da alheri wa duk wanda aka samata kidney dinshi, yusuf yaki motsawa agefenta itakuma idonta zur akansa shima hakan jiyake kaman ya hadiyeta, inna ne suka shigo anma duk dahaka yusuf yaki matsawa saidai kowa yagaidata daga nesa.

Sufyan daya shigo yaganshi yasan meyakeji donhaka yajashi dakyar yace yaje yahuta ganin sufyan yadage yasa yusuf yanufi dakin likitan ranshi abace yatuna da tsohon bacin ransa, likitan yazaro ido don yaji labarin yusuf yasan mesuka aikata donhaka tuni yashirya dazuwansa , zama yayi akan kujera sannan yace masa "inaso infarajin bayani daga farko meyasameni , me kuma kuka shuka da gimbiya kuka min karya!, " yayi gyran murya sannan yace "yarima duk abinda yafaru kadaukeshi kaddara tun asali dana dubaka kai kanka bakada ishesshen lafiya, abubuwan dakake sha sundan maka lahani kadan, kidney dinka basu da lafiyan dazaka bawa wani, ana cikin haka kuma mahaifiyarka ta isar da sakon karmu cire, dafatan zaka fahimceni" yusuf bai ce komi ba yatashi yanufi kanshi fitsarine likitan baiyi a wando ba domin ya mugun tsorata yusuf yariko kwalan rigansa sannan yace "daga yau duk abunda yashafi aliya, babu wasa aciki inaso kasan dahakan" Juyawa yayi yabar office din dakin da aka kwantar da abdullahi yanufa idonsa biyu yanaso asallameshi anma likitan yace bayanzu ba saiya kara samun sauki donhaka duk asibitin tahau masa kai,

Yan biyu ne hassana da hussiena suka shigo kowacce taci kwalliya dakin da abdullahi yake aka nuna masa suka gaysheshi da jiki sannan suka ajiye ledan hannunsu yusuf yafita alokacin, harzasu wuce abdullahi yace kucika ladanku mana ku gayda aliya, hussiena kaman tace a a anma tana kunyan abdullahi donhaka tace masa toh, dakin da aka kwantar da aliya suka nufa, idonta biyu bakowa a dakin sai inna suka gaysheta kamar abun arziki sannan suka nufi gadon aliya hassana tagaidata yayinda hussiena ke mika mata sakon harara, aliya murmushi tayi don tasan dalili, can dai hussiena takalli tareda cewa "anma kinsan yarima yayi asaran kudin tara? Ace wannan zaicire sauran kodan shi kwaya daya yamika mata? Dasunan soyayya? Mayya duk yaran sarkin kin mamaye" inna ce tanufo kansu tareda katseta tanacewa "kuyi hakuri baason daga mata hankali" aliya ce ta katse ta tareda cewa "wani yarima?" Hassana taja tsaki tareda cewa "wanne kuwa abdullahin dakika nakike wa" wani nauyi taji akanta kaman ansauke mata dutse


To be continue....

Godiya ga Benaxir Umar da ta rubuta.

Wednesday, 29 June 2016

Halaccin Sarauta episode 30 Wednesday day 29th June

Continuation of Halaccin Sarauta episode 30

Read the previous Halaccin Sarauta episode 29


Ayadda ya isa kofan gate din sukansu dogaran saida suka matsamishi sunga yadda yashigo da motan, abude yabar motan da mukullin ajiki yashige cikin gidan a birkice fannin falmata yanufa a harzuke dogarai dasuke kofan gun suna ganinshi suka matsa masa don ayadda yazo kaman guguwa ne ta tunkudoshi tana zaune a falo rike da waya a kunnenta yashigo fuskarshi a daure bata taba ganinshi haka ba, tuni tasha jinin jikinta ta tabbata angaya masa, ajiye wayan tayi tana kallonsa,cikin hushi da zafin murya yace "inaso kibani hujjanki nashiga rayuwata, kibani hujjanki na takurani," dakewa tayi duk da ta tsorata "bakayi girman da zaka yanke wani hukunci dakanka ba!, inbanda dolonci irin naka nadan fari tayaya zaka cire wani fannin jikinka a matsayinka na dan sarki, sannan kuma sarki anan gaba kace zaka bawa baiwa?!"

Murmushi yayi wanda tafi kuka ciwo yace "yanzu na fahimci inda kika dosa, toh inaso yau kisa aranki bakida da , sarki kuma kike can kinemi wanda zai cika miki burinki, baiwa???? Itace ta nutsar dani, takuma ladabtar dani abunda ke kika gagara yi!" Yana fadan haka yajuya yafice, ji tayi kaman ya watsa mata ruwan zafi, salati tayi tana rike kirjinta, yau dan cikinta shine ke mata gori,haryazo corridor yaga jakadiya yasan ita aka aika tafadi sakon, daya makuro wuyanta wani kara tasaka domin a tsammaninta zata leka lahira ne, dakyar dogarai suka karbeta suma yakoma kansu akarshe rikeshi akayi don abunsan yafara dawo karamin hauka, kuka yakwanta wiwi yanayi a daki tunda tahaifeshi baitaba tur da halayenta irin na ranan ba, yayi wadaran da halin mahaifiyarsa akan meyasa bazata koyi nagari ba don itama nata suzama nagari,

Matar abdullahi tafarka jikin nata da dan sauki gashi cikin mai laulayi ne, duk tadamu kishin mijinta yashiga ranta duk da yamata bayanin cewa arashin na mutane ne yabada nasa, toh ita tambayan anan shine yasan guda daya ne yasaura mishi akan meyasa zai bayar? Yana nufin zai mayar da ita karamar bazawara! Lallema duk tabi tadamu jira take yawarke don tasauke masa farillai da mustahabban rashin mutunci,aliya sai sha daya na dare tafarka da salatinta tafarka tuni sufyan ya kirkira su kowa yanufo gun dama abdullahi na asibitin, sai inna, yusuf kuwa yanacan shima bakanshi, bude idonta taga sufyan akanta duk tarame tayi kashin wuya, lebenta ya bushe idonta ya kumbura yayi jaa yariko hannunta yana murzawa idonsa fir akanta, dakyar tadan murmusa sannan tabude baki zatayi magana anma takasa, yace mata tayi shiru kartayi magana Allah yabata lfy. Inna ma sai faman tofa mata addua take taki motsawa daga baya kuma tamike ta dauro alwala tafara sallah tana addua Allah yadaga kafadun aliya, baccine yakara kwasan aliyan sannan yazauna agefe shima ya gyangyada sai asuba dayaji kiran sallah sai ya mike yafita dauro alwala yanufi masallacin asibitin, inna kuma a dakin tayi sallah, aliya sai karfe goma ta farka yusuf shima yashigo anma kana ganinshi kassan yana cikin damuwa,idonsa radau radau ya kumbura, yazauna agefenta itama kallonsa take yariko hannunta jikinsa yayi sanyi lao itakuma zafi kaman wuta, batayi magana ba har lokacin tagagara magana, yusuf kuwa shi dazaa cire zafin yakoma kansa dayafi kowa farin ciki, yazura mata ido alokacin likitan yazo dubata donhaka suka fita bashi wuri. Dawowansu dakin bayan likitan yagama yusuf yazauna agefe. Can dai aliya ta daure sannan tace "wayaban kidney dinshi?

To be continue....

Godiya ga Benaxir Umar da ta rubuta.

Monday, 27 June 2016

Halaccin Sarauta episode 29 Saturday 27th June

Continuation of Halaccin Sarauta episode 29

Read the previous episodes click HERE

Yusuf kuwa tun yana jira yaji bazai iyaba, kuka yake wiwi sufyan yafara lallashinsa anma duk dahaka yusuf yagaza yana kuka yana cewa "aliya kitashi, namiki alkawari bazan kara shan wani abuba, aliya na nutsu nadaina duk abunda nakeyi, aliya wlh inasonki, dukkan kai nason dukkan ki, "jin abun yadawo sumbatu yasa sufyan yabashi gu, antyn abuja da inna dakuma yanuwa kakkani duk suna zaune ana jira likita yafito yace ansaka mata lafiya nima benaxir ina tsaye agefe inata adduan Allah yasa ayi aiki lafiya Bayan awanni kadan sai gashi likitan yafito sun bazama kanshi kaman zasu cinyeshi, anan yabukaci sufyan yazo nan da nan yusuf yabisu likitan zaiyi magana sufyan yace "badamuwa ana tare" binsa sukayi office suka zauna sannan yafara bayani "anyi aiki lafiya alhamdulilah jikinta kuma yakarba, yanzu bata tashiba don Allah duk wani abu na tashin hankali kar ayi agabanta, sannan inaga kar agayamata wa yabata kidney dinshi yanzu harsai ta warke," anan sufyan da yusuf suka mishi godiya sannan yamusu bayani akan akwai nurse dazatazo tamusu magana, suka fito ahaka sannan inna tamike tareda tambayan sufyan yace anyi lafiya, dakin abdullahi yanufa don suyi magana anan yace masa ai anyi aiki lafiya anma bata farka ba, yayi murmushi sannan yace "ina rokon alfarmarka" "Na mefa?" "Don Allah kasamu kayiwa yusuf magana da duk wanda yasan maganan nan wanda kasan zai iya fadawa aliya, don Allah kar afada mata nina bata kidney acemata siya akayi, " "Anma kasan dole tasani ko? Tunda yanzu bakamn da ba, dole kana yawan zuwa asibiti maganan gari baya buya" "Nidai kamin wannan alfarma abari sai bayan raina afada mata, don fada mata yanzu zaisa tafara diddigi banaso tagane cewa nine masoyinta dana guje mata,"

"Ba gudu mata kayiba, ita tagudu maka kadena fadan haka" "A a nidai don Allah kar afadawa kowa maganan nan tawuce, karta sani" Dahaka sufyan ya yarda bayan fitowarsa yakira yusuf yamasa bayani anma yaboye masa dalilin dayasa abdullahi yayi haka shidai yusuf yasan cewa abdullahi na son aliya ne inbahakaba bazai taba bada wani fanni na jikinshi yazabi mutuwa akan rayuwa ba, dahaka sufyan yabarshi harzai fita yaci karo wani likita wanda haushinsu yakeji alokacin akan meyasa zasu yadda abdullahi yabada jikinsa, ba gaira a dlili ya makuro likitan tareda tambayansa dalili, likitan yana neman hanyan kwacewa karya mutu don numfashinsa daukewa takeyi, dayaga zai wahala yace "gimbiya falmata ce tahana mu yarda kabayar" ahankali yasake wuyan tareda cewa "mekace?" "Gimbiya falmata ce ta aiko da wasika akan duk wanda yacire wani bangare na jikinka abakin aikinsa" Sakeshi yayi yabar corridor din mota yanufa yayi wani wawan burki yayi hanyan fada

To be continue....

Godiya ga Benazir data rubuta wannan labarin.

Saturday, 25 June 2016

Halaccin Sarauta episode 28 Saturday 25th June

Continuation of Halaccin Sarauta episode 28

Read the previous episodes click HERE

Sufyan ne yarikeshi tareda cewa "wuce muje" bai iya tuka motan ba hakan yasa sufyan yafito dashi yakoma yafara tukawa, asibitin suka koma dasauri suka shiga, alokacin matan abdullahi kuka take sosai hankalinta yatashi nan da nan magana yazaga gari, har fada tunda yakolo take hankalinta baitaba mummunan tashi irin na wannan karon ba, a gigice tabar fadan ta umurceta da akawota asibitn, kuka take sosai.

Alokacin data iso asibitin yacika tam, mutane saisukaja gefe kawai suna kallon ikon Allah, yakolo ne ta bukaci tashiga dakin anan likitan yasa aka shigar da ita, don yace mata dan nata yanada jiki mai kyau tun awa biyu dasuka wuce idonsa biyu, hankalinsa akwance duk da zafin ciwo dake damunsa, cikin zafin murya da raunin zuciya tace "meyasa zakayi haka abdullahi? Baizama dole don zaka gwada mata kana sonta kasa rayuwarka a hatsari, haba abdullahi yanzufa kai rayuwa batada amfani agareka zaka iya mutuwa akoda yaushe aduk lokacin da jikinka tagaji da wannan injin, haba abdullahi!!"

Tunda yake baitaba jin mahaifiyarshi takira sunanshiba yasan cewa ta tabu matuka, donhaka yamika mata hannunsa tarikoshi gam kaman bazata sakeba "tun ina karami kin koyamin muhimmanci rikon alkawari da cika alkawari, a tarbiyan gidanmu na sarauta natashi naga mahaifina yana cika duk wani alkawari daya dauka , meyasa nima bazan kwatanta hakaba? Shin bakimin kwadayin aljanna? Shin bakimin kwadayin rahaman Allah? Don Allah ki kwantar da hankalinki, nasan ina son aliya anma cika alkawari shine musababbin bata sauran kidney dina, inban bataba duk nan babu mai bayarwa, sufyan nashi ba lafiya, yusuf kuma nazo wucewa naji gimbiya falmata ta aiko ace mishi karsu yarda subada na yusuf ko abakin aikinsu, kuma nasan cewa ko batayi magana ba bazaitaba yiwuwa yusuf yabada nashiba, tunda kinga yana shaye shaye bazai yiwu ace kidney dinshi lafiya lao ba, annemi nasayarwa baasamu daidai nataba, dole nacika alkawarin dana mata nacewa koda raina zanbayar don naceci rayuwarta, kitaimaka ki bano kwarin gwiwa don insamu inwarke, mutuwa kuwa inna mutu lokaci nane babu wanda yake mutuwa ba lokacinsa ba, " yakolo kuka take sosai tareda hamdala azuciyanta tana godewa Allah dayabata yaro mai ingantarcen tarbiya, mai kyan hali tunda take bata taba ganin abdullahi yayi alkawari yasaba ba, mutum ne mai daraja dan adam, taja numfashi sannan tace "nagode sosai daka fahimtar dani, Allah yarayamin kai yabaka tsawon rai yataimakeka,

Allah yadaga kafadunka" anan tamike tabar dakin kuka yacita sosai balle matarsa karshe gado aka bata anan likitan yasamu tanada ciki ga murna ga bakin ciki, yusuf kuwa yana makale a gefen dakin tiyatan dazaayiwa aliya, yaki motsawa azamansa agun falmata tasa akirashi yakai sau biyar daga karshe tashi yayi yawanke dogarin da mari saida aka fita dashi yace karsu dameshi, sufyan kuwa zuwa yayi yasiyo abubuwan dazaa bukata na abdullahi da matarsa, Mai martaba sarki yaji bakin ciki sosai musamman da falmata tace masa wa baiwa yabada kidney dinsa, shikadai a fada yarinka fada, daga baya ne da yakolo ta koma gida dakyar a kukan nata sai ganin mai martaba tayi akanta yana shigowa yafara fada akanme zatabarshi yafita haryaje yabada jikinsa ganin yadda yake fadan tasan cewa falmata ta shuka wani makircin anma yazatay? Dole tamai bayani hakan yasa tazaunar dashi tamai bayani dalla dalla tana kuka yaji tausayinta sosai yakuma ji son dansa yakaru, rungumarta yayi yana lallashi.

To be continue....

Godiya ga Benazir data rubuta wannan labarin.

Monday, 20 June 2016

Halaccin Sarauta episode 27 S Monday 25th June

Halaccin Sarauta episode 27

To read the previous episodes follow the link HERE 

Tunaninsa duk yajuya, alokacin suka nufi fannin da aka kwantar da sufyan abdullahi ne ke zaune agefensa inda yake zura masa ido sufyan yayi murmushi sannan yace "karka damu, zageni kawai raina baxai baci ba," hakan yasa abdullahi ya makeshi dakarfi tareda cewa "soko, wawa!ka cuceni wlh, kacemin harda ita a rasuwa meyasa ka boyemin tana raye?"sufyan bai damu da zagin ba yace "yazama dole ne,dole in boye wa duniya wacece ita, ko so kakeyi itama abimin ita akashe?" Shidai abdullahi baice komi ba yasan cewa abun yanaciwa sufyan rai shiyasa baiyi wani rikici ba har suka sallameshi daga bed rest din dasuka bashi alokacin sukaje dubata, tafarka anma ta jigata sosai, har ranta taji haushi asalin haushi taji don tabbas tasan cewa tanada matsalan kidney tanemi nasayarwa ko zata siya asaka mata tafasa daga baya acewanta kar tazo tafara ciwo bata cika burinta ba, gwara tagama idda cika burinta kafin ta kwakulo wani ciwo gashi yanzu sun nemo, kuma sunaso sucire tasan duk yadda zatayi suhakura bazasu hakura ba dole tabari su saka, fatanta Allah yatada kafadunta don ta cimma burinta Sufyan ne da abdullahi suka shigo dakin ta tsaya ne taga ko zataga yusuf bata ganshiba nan da nan zuciyanta ya sosu sosai, abdullahi kuwa saiyake ganinshi kaman bakon mutum agareta, kaman bakon fuska, tayaya zaifara fuskantarta?

Shikam yadawo ruwa tsundum!, zama sukayi agefe sufyan yariko hannunta cikin tausayi, yanason kanwarsa gani yake itace sauran bangaren jikinsa, ganin basuda niyya magana ta bude baki da kyar sannan tace "meye haka kaman na mutu!" Sufyan yayi murmushi tareda cewa "bazaki mutuba ko raina zan iya cirewa nabaki don na sadaukar dakaina agareki"abdullahi hawaye ne ke zuba masa a ido anma yanata kokarin yaga yadanne yashare saboda kar agane, duk lokutan dasuka kasance tare suna yara yatuna, yatuna lokacin daya mata alkawarin zama da ita ko wani hali na rashi ko samu, yamata alkawarin taimakonta cikin kowani hali ko da kuwa zai rasa ransa ne, cikin sanyin murya yace "yajikinki?" "Dasauki ranka shi dade" a karo na farko kenan dayaji wani iri data kirashi haka yasan ada takan ce masa "yayana" bazai iya zama ba bai amsata ba yafice yabar dakin waje yafita yashiga motarsa kuka yafarayi sosai, tunda yataso yayi wayo baiyi kukan dayayiba, nadama duk ta isheshi, toh ni benaxir damuwan meyakeyi?

Aiba laifinsa bane, yusuf ne yashiga dakin alokacin inna tagama jimaminta tana zaune itama agefe shidai sufyan yaki motsawa, yusuf yazauna agefe tareda cewa "yajikin?" Bata amsa shiba anma ta gyada masa kai, hakan yasa yaja gefe yazauna duk yadamu, likitan ne yashigo don dubata bayan dube dube yace sufyan yazo su gwada kidney dinshi, yabi likitan inda sukaje akayi scanning aka duba kidney dinshi da lafiyansu sannan ko shima zai iya badawa wani bayan dogon bincike likitan yakirashi kanshi a sunkuye yana cewa "kayi hakuri sufyan, bazaka iya bawa aliya kidney dinkaba saboda kaima naka basuda isheshen lafiya," wani dogon salati inna tayi sufyan kam daskarewa yayi agun, yagagara motsi shikan hankalinsa yatashi, yazaiyi da rayuwansa? Anan yafara rokon likitan yakawo dabara ataimakawa yar kanwarsa anan likitan yakawo shawarar akira yusuf, nan da nan suka kirashi atake ya amince zaibayar inda akace yashiga don amasa scanning shima, bayan ankammala likitan yace washegari zasuji result tunda dare yayi, hankalinsu duk yatashi innace ta kwana a asibitin abdulahi da yusuf suka koma gyda, ko yusuf dayaga falmata zata dameshi fitowa yayi yabar masu gidan, Washegari karfe tara anty ta iso asibitin yusuf, abdullahi da sufyan suma duk suna gun, likitan yakirasu inda yabawa yusuf hakuri cewa "yusuf you are not a donor donhaka bazaka iya bataba, kidney dinta bazai karbi naka ba" tunda sufyan yake baitaba fuskantar tashin hankali irin wannan ba baisan sanda yafara fidda hawaye da gumi ba, yusuf kam kuka yake wiwi, yarasa yazaiyi anan duk suka fito abdullahi yagagara tafiya, hankalinsa yatashi office din yakoma tareda cewa "dr. Kidney dina guda dayace tayi saura, ko akwai hanyan dazan iyabata ? Tunda kunce agobe kukeso!," Likitan yakalleshi alaman mai tababben hankali sannan yace "kayi hakuri kanaso ka mutu ne?" Cikin tsawa abdullahi yace "meruwanka da mutuwa ko rayuwata! Kagayamin hanyan dazanyi"cikin tsoro likitan yajawo files dinsa sannan yace "Inhar zaka bada sauran kidney dinka zakadawo bakadashi ko daya, toh munada dialysis machine wanda yake aikin da kidney yakeyi, dashi zakana amfani har lokacin da jikinki zatayi resistn ," abdullahi yayi hamdallah sannan yace duba kagani ko zan iyabata inyaso kacire ayau dinnan kanemo danwanka zanbiya ko nawane, kusamu kusamata kozata sami lafiya, sannan karka yadda kafadawa kowa!"

Likitan ya tsorata shikam yakasa gane kansu, gashi dai danuwanta bazai iya bada nashiba, yusuf kuma falmata ce ta aiko wa asibitin wasika cewa karsu yadda su dauka nashi susawa wata banzar bawa ko dukkansu zasu rasa aikinsu, hakan yasa duk suka tsorata suka cemasa nasa bazai karbu ba, ga abdullahi mai mata anma ya yanke shawaran yahakura da duniya, dahaka yaduba yaga komi daidai atake yayi magana da likitan dazasu cire, adaren ranan suka cire masa kidney dinshi kwaya daya, masha Allah sadaukarwar soyayyaya da cika alkawari tabbas abdullahi yanuna nagarta da hallacin sarauta, yanuna cewa inhar baicika alkawari a matsayinsa na masoyinta ba albarkar sarautar gydansu zaisa yacika, yagwada mata cewa agydansu yatashi da nagarta, baimanta da alkawarin tun suna yara ba yau yacika. Yacika mata alkawarinsa nacewa zai tsaya agefenta, zai taimaketa koda kuwa zaizama ajalin rayuwarsa, acikinmu mutane nawane suke cika alkawari? Sufyan kuwa yana wata duniya daban don neman kidney dazaasa wa aliya shida yusuf sai kiransu akayi aka sanar dasu abdullahi yabayar yusuf dayake tuki saidayayi wawan reverse yatsaya sanin cewa abdullahi kidney dinshi dayace tarage suna nufin yabada wannan? Lalle kam akwai rikici, abdullahi nason aliya? Innalilahi yazayi?

To be continue....

Godiya ga Benazir data rubuta wannan labarin.

Saturday, 18 June 2016

Halaccin Sarauta episode 26 Saturday 18th June

Continuation of Halaccin Sarauta episode 26

Read the previous episodes follow the link HERE

Cikin wani yanayi na fargaba tace "yarima?" Dasauri tanufeshi shikuwa yanufi inda aliya take ya kunce igiyan da aka daureta dashi, ji yayi kaman ya rungumota ko zatasan halin da zuciyanta take ciki anma babu yadda ya iya, tuni kuwa abdullahi yashigo filin shima riketa yayi suka dagota wanda kowa saida yayi mamaki kenan aliya tasan dukkansu? Bilki ce tanufesu don riko aliya, sufyan ma gun yanufa nan da nan akasata a mota yanufi asibiti da ita, yayinda falmata ta yi umurni da a watse nan da nan yusuf yace baigama ba yanada magana, hankalin falmata yatashi tasan cewa asirinta zai tonu donhaka takara daure fuska anma yusuf bai saurareta ba, yakira likitan dasu abdullahi suka kawo mishi da likitan da falmata takawo, yacewa likitan falmatan yamasa bayanin meke damunsa cikin tsoro yace "zazzabi ne da rashin bacci,", yakalli likitan da sufyan suka kawo masa sannan yace masa "meka samu yake damuna?" "Allurai ne akayi ranka shidade da dan kwayoyi "

Yusuf yamike yahade rai tamkar sarkin dayake shirin yanke hukunci "kukama minshi harsai yafadi dawa yahada baki aka sashi abunda yayi," nan da nan dogarai suka kamashi, anan yahado da tsohon da aka kama wanda yake cewa tabbas shi mai kama mayune kuma aliya ma mayyace ita tacinye iyayenta, dukka yasa aka kamasu sannan yanufi fanninsa wanka yayi da zummar yabi aliya asibiti saidai fitowarsa yatarar da mahaifiyarsa tana jiransa, bai kalletaba balle yanuna yasan tana gun harta gaji donkanta sannan tace "in nina haifeka kasakesu" Wani kallo daya mata itakanta saidata tsure bai kulata ba don tunda yake itakanta bata taba ganin bacin ranshi irin na ranan ba, kaya yasa yafito don ji yayi yatsani munanan halayyan mahaifiyarsa don batada hali ko kadan tabari son mulki da son zuciya yarufe mata ido, bayason halin mahaifiyarsa ko kadan yasan shima da halinsu daya anma haduwarsa da aliya yacanja, yadawo cikakken mutum yadawo mai tausayi yakuma san darajan dan adam, yanzu yasan meya keyi kuma ya gode Allah daya hadasa da aliya akullum yana kara kaunanta sonta daban ne, dasauri yakunna motan sannan yafice daga fadan, asibiti yanufa wanda aka kwantar da aliya wacce ta gigice, sufyan duk tunaninsa karya rasata, haushin duk yancikin gydan yakeji don gani yake aliya zata iya rasa ranta, Allah kadai yasan kukan dayake a zuciyansa, tunaninsa Aliya ce kadai tarage masa yazaiyi insun rabashi da Aliya.

Donhaka duk tunaninsa ta tsaya cak yusuf ne yashigo a rude yana tambayan ina aliya, abdullahi ne yamasa bayanin cewa sunbata gado suna dubata,numfashi yaja yazauna yadafa kansa nauyi yaji kanshi yanayi, don shikanshi wankan dayayi ne ta taimaka masa yaji karfin jiki, sunfi awa azaune kafin likitan yafito nan da nan suka mike inda yace musu tasamu kidney problem don kaman anmata wawan bugi agun, kuma gaskiya dukka biyun sun lalace ana son acire kuma abata guda daya, bayan haka anason jini sannan kuma tabugu sosai akanta dole ajira aga farkwanta suyi adduan Allah sa tatashi lfy kar asamu wani matsala,sufyan dafa kai yayi ya tsuguna agun saiga hawaye suna zubowa, abdullahi da yusuf wanda shima ya rikice kallomsa suke, kishine yashiga ran yusuf akanme sufyan zai damu? Meye hadinshi da aliya? Atake yace likitan yacire nasa inyazo daya, anma sufyan nan da nan yamike tareda cewa muje aduba kidney din, da jinin , yusuf wani harara yasakar mishi domshikam ji yayi hankalinsa yatashi har bari hannunsa yake, likitan saiyaga kaman abumsun gasane, donhaka yace waye yafi kusa da ita? Yusuf yayi caraf yace "nine masoyinta" Sufyan bai kalleshiba sannan yacema likitan "muje ! Ni yayanta ne uwa daya uba daya!"

Ba yusuf ba hatta abdullahi dake kallon su sai daya tsorata wayan hanninsa yasake a kasa, tunaninsa ya tsaya cak, ya cukumo sufyan "kai dabban wani gari ne? Don kawai kana sonta zakace kai danuwanta ne?" Inna wacce tashigo asibitin a rude taga sufyan wanda yakirata yamata bayani tanufo kansu dasauri tanacewa "sufyan ina kanwarkan take? Yau munshiga uku innalilahi" yusuf sakeshi yayi don ya mugun tsorata, azatonsa yasan wacece aliya ashe yaudaran kansa yake baisan komi akantaba, jan jiki yayi gefe tareda zama akan kujera yayinda sufyan yanufi dakin likitan don samun karin bayani gameda kidney dazai bayar inda likitan yasanar dashi cewa dukka biyu sunsami matsala sun lalace donhaka dole acire asamata wani ko guda daya tasamu tayi surviving, tunda har kumbura tanayi wanda sai alokacin shi sufyan yalura dahakan shidai yasan yaga tacanja baiyi tunanin wani abuba tunda baidade da ganintaba anan yace shi yayanta ne uwa daya uba daya aka bashi duk wani fike dazai cika, yasa hannu sannan yace afara duba jinin , jininsu yazo daya atake aka diba , leda biyu yabayar yakwanta don yahuta bayan kwana uku zaa cire kidney dinshi daya abawa aliya, har kuka saidayayi akan gadon, yanason yar kanwarsa Bangaren yusif kuwa yarasa mezaiyi murna?haushi?takaici? Dole dai yayi dukka dole yayi farincikin cewa sufyan yayanta ne ba aure a tsakaninsu balle yadamu , nabiyi kuma dole yaji takaici da aliya taboye masa asalin cewa sufyan yayanta, tabbas hakane abdullahi yasanar mishi sufyan dan marigayi galadima ne anma baitaba kawowa aliya ba, lallai shi soko ne, meyasa aliya taboye mishi wannan bayan yasan babban sirrin ta balle wannan, shidai yanzu duk yarude damuwansa tafarka Inna kuwa duk ta tsure duk yanuwa na nesa saidata kira tasanar musu, antynsa ta abj ma tace zata biyo jirgi ta taho washegari, anan yusuf yasan cewa lallai aliya tanada gata, anma meyasa suka barta take bulayi agari?

Abdullahi kuwa ayanzu yatabbatar da inda yasan aliya. Tun randa yafara kallonta yasan cewa yasanta awani gu!, tabbas itace kanwar sufyan wacce suke wasa da ita ya kyalla yace yana sonta, wacce yanemeta yarasata, akacemasa tatafi abuja dazama, wacce itace first love dinshi, ba shakka itace shiyasa duk lokacin dayaganta cikin wani hali baya sharewa saiya taimaketa, tabbas itace innalilahi yazaiyi? Yanzu yafarajin sonta danye, ruwa tsundum yadawo, yazaiyi da yusuf? Yazaiyi yatabbatar mata dacewa itace?

To be continue....

Godiya ga Benazir data rubuta wannan labarin.

Wednesday, 15 June 2016

Halaccin Sarauta episode 24


Previous episodes of Halaccin Sarauta episode 24

Continuation of Halaccin Sarauta episode 25

Gabanta fadi yake don babu irin tunanin dabatayi ko wanene ba, dahaka suka isa fada taga bayanda tasaba ganin mutane ba, andan cika sosai, fannin falmata aka nufa da ita inda taana ganinta ta taso ta wanka mata mari umma uwar soro ne tayi sauri taja aliya wacce tarike kuncinta cike da takaicin abunda yasameta batasan metayi ba ankafamata mari, falmata cikin fushi take cewa "duk wanda ke da hannu acikin wannan aikin kuhado min dashi," ahanyan fita da itane taga sufyan da abdullahi suna tsaye ganinta da yayi yasa ya tsure anma bai gwadaba don kar wani ya tsammace wani abu, yaja abdulllahi gefe tare da tambayanshi meya faru? "Kasan harkan mata da matsala, nagayawa yusuf yabar yarinyannan saboda abunda zai jawo mata, mahaifiyarsa batada shariya, yaki yadda, yanzu yazo yakwanta ciwo tun ast week, anma ciwon yayi tsanani ne shekaranjiya wanda dogaransa sunce daya dawo daga gidan aliya ne yakwanta. Kuma sumbatu yake yana kiran sunanta, hakan yasa mahaifiyar tace ko aliya tamishi wani abune, wai mayya ce tanason cinye mata da, " "Subhanallah" "Yanzu dole munemi hanyar fidda aliya daga wannan matsifan narasa meya dawo da ita garinnan" "Muje muga gimbiya" Suka nufi fannin gimbiya yakolo inda suka mata bayanin abunda ke faruwa hankalinta yatashi sosai, anma babu yadda ta iya bata isa tasaka baki aciki ba, don baa haka, yazama dole tanemi mai ceton aliya hakan yasa tafito don zuwa ganin aliya wanda akasa a cage, aliya idonta ya kumbura yayi bul don tasha kuka, ita badamuwanta abunda suke mataba damuwanta shine yusuf yawarke ko zata gwada masa irin son datake mar, kodataga gimbiya tuni kukan yakaru,gimbiya ta yi umurni wa masu gadin dasu fice zatayi magana da ita suna fita tariko hannunta "Aliya meya faru? Kigayamin gaskiyan abunda kika sani" Cikin kuka aliya tabata labarin abunda yafara faruwa tundaga tsohon gidanta, zuwa haduwanta dasu hassana da hussiena dazuwamshi data koreshi da ilya, dakuma zuwanshi na biyu shekaranjiya kenan sannan tacigaba dacewa "wlh ranki shi dade ni ba mayya bace,jinina a tsarkake yake," Gimbiya yakolo taji tausayinta anma babu yadda ta iya donhaka tace "bazai yiwu naceceki ba, dole dole shi zai ceceki idan yamike akan gado, inhar bai mike ba, zata iyasakawa a illata ki"hankalin aliya yakara tashi bata taba jin mutuwa zamzam haka ba, tagama tsorata tarasa ina zata saka ranta, gimbiya tasamu tadan lallabata kafin takoma fanninta ta ai akira bilki, ta umurceta datana kai mata abinci tace injita, takira abdullahi da sufyan ta bukaci suje suga jikin yusuf din ko zaagane meke damunsa sun nufi fannin sa, suka tarar da likita ne sai bayi guda biyu, sufyan yazauna yadan duddubashi kasancewar yanada dan ilmi akan lafiya,yakuma tambayi likitan shidai likita yace jininsa tahau abinda yagani kenan, sufyan yadanyi dube dubensa sannan yaja gefe yazauna kusa da abdullahi yana cewa "nifa inaga akwai abunda ke damunsa yana boyena, its lyk akwai weak heart, mezai hana akaishi asibiti agani, abdullahi ya amince da shawaran, nan da nan ya umurci da azo akai yusuf asibiti , falmata wacce take fanninta tuni tafaso dakin hankali a tashe tana cewa " iiiiiina kuma zaku kaishi?" Daga yanda take jan maganan sufyan yagane cewa tabbas batada gaskiya, abdullahi yadaure fuska sannan yace "asibiti zamuje suduba jikin dakyau" "Babu inda zaku kaishi!" Cikin tsawa tafadi haka don saida hankalin bayin yakoma gun kowa ya tsaya jungum jungum, ganin basuda niyya yasa abdullahi yariko yusuf din dasauri sufyan yarikoshi alamun yabari karya rikoshi haka suka barshi akan gado suka fito domin kuwa falmata ta kasa ta tsare Bilki kuwa dataje kai abincin basu barta tashiga ba dole takoma tasanarwa yakolo abun yaci mata rai anma babu yadda ta iya dole ta san yadda zaayi a farkar yusuf kamin wani abu yasami aliya, sufyan kuma samu yayi ya lallabi abdullahi suka shiga gari babban asibiti suka dauko likita yazo da kayan aikinsa a fannin abdullahi yasauka wani daki da aka ware masa, suna jira dare tayi donsu cika aikinsu inhar basu magance matsalan adaren ba washegari zaa iya zartarwa aliya hukunci domin falmata tasa annemo hujjoji nacewa aliya mayyace kuma ita take illatashi inhar baakasheta ba yusuf bazai tashi daga sumbatun dayake ba,saida suka bari kafa yadauke sukaja likitan suka kaishi fannin yusuf suka rufo kofan, yayi bincike sosai yagano cewa kwaya aka bashi wacce tafi karfin kwalkwalwarshi hade da allura, saboda kasanceear aliya ce aransa yasa yake sumbatar sunanta, yadanyi dube dubensa sannan yace zaiyi alluran dazaiyi reversing dinshi, anmishi allurai kwaya biyu anma likitan yanuna musu cewa sai bayan awa hudu ko biyar yatashi hakan yasa dole suzauna agun, dukkansu babu wanda ya runtsa yusuf baitashiba sai hudu na asuba nan da nan suka lallaboshi yazauna suka watsa mai ruwa zai fara matsifa abdullahi yatoshe mai baki sannan yace yayi shiru yaji, cikin basira suka mai bayanin abunda ke faruwa sannan sukace hanya dayane don ceton aliya idan safiya tayi yacigaba da yadda yake inyaso idan antashi hukunta ta yafito yafadi gaskiya shikam tuni hankalinsa yatashi jin cewa aliya na cage saboda shi, zuciyarshi na radadi mikewa yayi waizaice yadaukota suka danneshi dakyar suka lallabashi ya yarda, kafinnan suka wuce fannin abdullahi don yin alwala sutafi masallaci alokacin ankira sallah Dasafe aliya idonta yacika ya kumbura ganin cewa yau komi zai iya faruwa da ita, taci kuka harta koshi ta godewa Allah,karfe goma saiga dogarai inda akaje da ita mahukunta, gurin da ake hukunta duk wanda yayi laifi acikin fada, ta sunkuyar dakanta ayayinda umma uwar soro taketa bayanin abubuwan da aliyan tadauka daga karshe tace "zaki fadi gaskiya ko ki fuskanci hukunci, ke ba baiwa bace da an miki hukunci mafi tsanani, sannan kinsan cewa hukuncin maita a masarautannan shine akashe mutum, donhaka kifadi gaskiya kisake yarima kisake kurwansa,donkar ki fuskanci tashin hankali, " Aliya kuka take sosai yayinda take kallon sufyan wanda ke mata alamun tayi shiru anma tagagara ganewa shikenan itakam yau mutuwa tazo mata, ta ina zata sake yusuf, gashi mintuna kadan aka bata tasakeshi, kukan datake harya hade zuciyanta alokacin. Kawai saiga yusuf yashigo filin falmata ita tafara tsorata tamike

To be continue....

Godiya ga Benazir data rubuta wannan labarin.

Monday, 13 June 2016

Halaccin Sarauta episode 24

Continuation of Halaccin Sarauta episode 24

Read previous episodes here  23

Tuni ya tallafota bashiri tamike "meye haka zaka rikeni" saketa yayi awh dama idonta biyu dakyar takoma don taji kunyan abunda tayi. Cikin borin kunya tace "mekazomin anan, ilya yana nan baiyi nisa ba" "Ki kira ilyan ko kasheni yayi ba inda zanje yau saikin gayamin menamiki,aliya hussiena ba budurwa ta bace so ake ahadamu da ita naki babanta abokin babana ne alh.hamidu, tuni tazauna tareda zaro ido, don ta tuna cewa sufyan yace mata alh.hamidu shine wanda suke tare da mahaifinta ran ajalinsa, dasauri ta sake fuska donkar ya fuskan komi "to ni meruwana?"

"Nidai don Allah kiyi hkr. Kezan aura kenakeso ke zuciyata take bida "nan yagama sumbatunsa anma aliya ko cikanka batace ba, yana fita tajawo wayanta sufyan takira yana dauka yace "menenee? "Kazo gida nasamu labarin alh.hamidu" bata saurayi mezaice ba ta kashe wayan cikin minti talatin saigashi ya iso "Aina kika samu labarin? Keda kike nanike a daki?" "Meruwanka? Yusuf yazo yana ban hakuri akan yan biyun dasuka min hauka ranan, wai yaran aminin sarki ne alh.hamidu" "Allahu akbar, duk bincikena banje kansa ba, don naga baida sarauta anma tazo gidan sauki, yaran yanbiyu ne? "Ae! Bazaka gane wanne bace hassana ko hussiena" "Tazo daidai zanyi soyayya da daya, kozan sami kusanci da mahaifinsu ko yakikace?" "Kayi da hussiena" "Munafuka don kihadani fada da yaronnan ko?" "Oho dai kaikasani" "Kedai ki tabbata babu wanda yasan alakanmu don anasani shikenan ansan kema yar galadima ce plans dinki duk zasu rushe" Ficewa yayi yabarta bai nufi ko ina ba sai fada fanni abdullahi da matansa, yasamu tarba sosai anan yagwada sa cewa yaga yar alh.hamidu kuma yanaso, abdullahi yayi farinciki inda yace wacce aciki? Sufyan yagwada cewa hassana yakeson aura, aikuwa nan da nan yafara murna yara masu hankali kayi saan mace dawannan yace su shirya daredare zasuje gun mahaifinta, Daredare suka sha manyan kaya suka nufi gydan alh. Hamidu wanda yakarbesu hannu biyu biyu, abdullahi yayi bayanin kudirin sufyan a matsayinsa na dan marigayi galadima, nan da nan alh.hamidu yace "hassan adamu? " Abdullahi ya gyada kai tareda cewa "ae shi"

"Masha Allah ashe zankara ganinka? Mahaifina aminina ne sosai, Allah yajikan rai" Dukkansu suka amsa da "ameen" "Ban isa naci amanar abotana da mahaifinka ba, donhaka in hassana ce nabaka!" Sufyan yanuna farincikinsa yakuma yi godiya ayayinda akace suzo washegari don ganin yarinya Ranan sufyan yayi bacci mai dadi ganin cewa yadauko hanyar bayyanar gaskiyan mutuwan iyayensa, Washegari yashirya cikin janfa ya sha turare sai kamshi yake suka nufi gydan shida abdullahi ayayinda aka musu iso, yana zaune kanshi a kasa gabanshi na fadi wanda shikanshi yarasa dalili tayi sallama ahankali muryanta cikin sanyi sannan tashigo, alokacin yadago yakalleta, tanada haske saidai bata da tsayi, kananun ido gareta anma tanada karan hanci, kyaunta dan daidai masha Allah, dama shi bai fiyeson bakaken mata ba, musamman wanda yafisu haske, abdullahi ne yatabashi tuni yadawo daga duniyan tunaninsa yafara amsa gaysuwarta,

kanta a kasa a zuciyanshi yace "anma aliya munafuka ne, yanzu wannan salihan yarinyan zatace taje tamata fada?wannan ai daga gani ba ruwanta salihar macece, suka gaysa sannan abdullahi yafara neman sasantasu itakanta hassanan tana fara ganinshi taji ya kwanta mata arai, domin kuwa sufyan yahadu namiji ne awaye, mai kyau da kwarjini taji ta narke da sonsa awansu biyu suka fito tarako su har gate sannan yakarbi numban wayanta, suna fita daga gidan tashiga dagudu gun hussiena wacce take labe take kallonsu tsaf suka hau tsalle da murna , su hassana anyi mijin aure, Sufyan kuwa yaki daina murmushi shikam sonta yake, karfa yagagara cika aikinsa harya ajiyeshi a gydansa sannan yakara fitowa yataho gydan inna, yayi hakanne donkar abdullahi yasan gydan saboda bacin rana, aliya tana kwance yashigo "Adarennan yaya meza kacemin?" "Ke. Tashi! Sharri zakiyima hassana ko? Yarinyannan yar salaha da ita ba ruwanta, "Ko dai taje ta nutsu don kissa irin na mata nikam kabarni bacci zanyi" fannin inna yaje yaci yakoshi sannsn yafice" Washegari aliya taci wanka tsaf tashirya cikin atamfa dinkin yakarbeta sosai ba kadan ba, tana zaune, sallama akayi wasu dogarai ne sukace wa inna ana neman aliya a fada Hankalin inna yayi dubu yatashi tazo fannin aliya "mekika yi musu?" "Babu , suwaye?" "Daga fada ana nemanki" tayi tunani iya tunani tarasa meya hadata dagun, tafito a sanyaye suka tisata agaba sai fada

To be continue....

Godiya ga Benazir data rubuta wannan labarin.

Saturday, 11 June 2016

Halaccin Sarauta episode 23

Continuation of Halaccin Sarauta episode 23

Read the previous episodes here



Aliya ta gyada kai wanda itakanta inna tasan cewa baikai har zuci ba, tana tantama dakyar ta amince anma tana tsoron abunda zaije yadawo idan aliya tayo bincike, bata cika son bincike ba itakam, tadai mike tabarta, tana fita aliya ta watsa ruwa tasako dogon riga tadaura dankwalin sannan tafito, inna ta kalleta "ina zuwa?"

"Kasuwa" ta amsa, inna takare mata kallo , saidai batace komi ba saikin dawo, aliya tasan mezatace donhaka ne ma tagodewa Allah datayi shiru, Allah yagani batason takuri rayuwarta ba tsanani, tafice saidai itakanta tasan tafita ne don taji gydan ya isheta batada dalilin fita, ganin me awara tayi tanemi gu tazauna tasiya ta murmuzashi a cikin ledan yadawo kaman kwado sannan ta tusa a jakarta, gydanta nada taje haryanzu baa shiga gydan ba, tashiga tazauna taci awararta ta koshi dama tana yawo da coke dinta, takora da coke sannan tafito da zummar takara gaba, hanyan fada tanufa kai tsaye batareda wani tunani ba, harta yanki kwana taga sufyan agabanta bai saurari mezatace ba ya damko hannunta ya wuce da ita basu tsaya ba sai awani lungu, "Meye kuma yaya?" "Bakida hankali ko? Ina zakije?" "Fada zanje" "Kimusu meye" "Na ga yusuf" "Mahaukaciya,wuce mutafi" Fizgan hannunta yayi suka isa bakim titi ya tsari keke napep suka hau sannan yayi kwatancem gun,

"Da kafana nazo, dakayi hakuri zankoma da kafana!" Bai amsata ba har suka isa yamikawa mai keken kudinsa sannan suka shige inna tana tsakar gyda taga yazo yawuce da aliya donhaka ta dauraye hannunta dama tana wanke kayan miya ne, tabisu don ganin meke faruwa, "Bakida hankali ne? Sau nawa zangayamiki aliya sau nawa zangayamiki ki fita hidimar fada!, kifita rayuwarsu, mutanennen baruwanki dasu, yusuf dinnan nagayamiki mahaukaci ne ki hakura dashi kinki yadda wato ga karamin dan iska" Inna tashiga dakin ganin yana matsifa yaki shiru tace "meyene yake faruwa? "Inna kiga shigan jikinta, yarinya gaba daya tadawo inyamura, aladan yarbawa, kinmanta akasan hausa kike? Kinje kin dauko dabian wasu kina mana anan!" "Yau nashiga uku zaku kasheni, meye zaka wani ce yarbawa, agarin yarbawa nazauna? Kaidai inzakayi matsifanka kayi ai gwara ni kai fa? Wayasan mekake aikawata, dogon riga ne ajikina meye aibunsa, ?" "Dakikasa dogon rigan shine zaki cire dankwalin?kin yafashi a gefe ,kokuma kisaka gajeren wando kina yawo a kasuwa, zanga ta inda zaki auru a garinnan, dawannan halin tashan kikeson auren dan sarki? Wazai baki? " Haushi suka bata itadai tasan ba laifi tayiba sunbi sunsa mata ido, wacce tasa atamfa ta rataye gyale awuyanta tarufo jikinta baaga laifinta ba? Saita datasaka abaya dayarufe jikinta don kawai tayafa gyalen?"nikuma nce maka zan auri yusuf ne? Ko na ce maka zanyi aurene? Basai ku aurar dani nagani ba" bai kulata ba yace "inna karta kara fita dawani shigan daya sabawa addini, wannan ai karamin hauka ne!" Yana fita tamike aranta tana cewa inga karamin beran dazai takurani , da tuntuni bakasan daniba saidana girma nasan darajana da mutuncina, tsaki tayi tamike akan kujera baccine mai nauyi ya kwasheta bata farka ba sai magrib tamike tadauro alwala tayi sallah sannan takunna tv duk da batagane mesukeyi don wani indian film ne tadai zurawa tvn ido sallama taji anyi anshigo tagane muryan anma tarufe idonta kaman tana bacci, yashigo yazauna ganin tana bacci yazura mata ido, yarasa yazaiiyi yanason aliya baikuma san meyasa takeson juya masa baya ba, saiyanzu yasan dalili da hussiena takirashi awaya yatabbata tazo tasami aliya ne, yadda yasan kishin aliya yasan saiyayi dagaske, ganin tanata runtse ido yaki ya tafi yasa tadanyi juyi.

To be continue....

Godiya ga Benazir data rubuta wannan labarin.

Monday, 6 June 2016

Halaccin Sarauta episode 21

Read the previous episodes here


Continuation of Halaccin Sarauta episode 21
Ina ma kowa barka da shan ruwa Allah ya amsa ibadinmu Amin.

Mai hijabin wacce itace hussienan takalli aliya cikin rashin tsoro tasa hannu itama tariko wuyanta, tareda cewa "ke angayamiki tsoron ki akeji?banza karuwa jaka dabba!" Aliya tasa hannu ta make bakinta tareda cewa "ki iya bakinki don banda mutunci" "Dama ina kikeda mutunci banza" Aliya fuzgan jikinta tayi tareda tattare komatsanta tafice tabarsu agun, gyda tanufa ta zauna akan kujera cike da bakin ciki da takaici, yusuf tasan zainemeta, anma wasu irin dabbobine wannan? Lalle zasugani shikuma yusuf zaixo yabata labarin suwaye.

Sufyan Ne yashigo kafanta yatare hanya ya mauje kafan yawuce hakan yasa ta tashi, tareda kallonsa "haba yaya dame zanji bakin cikin wancan yanmatan komeye?" "Wasu yanmata?" "Yanmatan yusuf bansansuba, kuma baitaba ban lbr ba" "Wannan saurayinkin baiyi kama da mutum ba, nima haka yamin hauka, bawannan bane takawoni, angama binciken wanda yayi kissan waziri ansamu cewa wata baiwa ce tashigo fadan itada mahaifinta waziri ya kwace gydansu da duk wani abu dasuka mallaka. Sannan yayi hanyan sanadin mutuwar matarsa, yanzu dai zaayi hukunci jibi, Kuma abincike na nasamo cewa akwai wani alh.hamidu shine kanin galadima na yanzu suna tare da baba randa zai rasu donhaka dole munemi hanyan dazamu sameshi donjin bayaninsa."

"Anma yaya fisabillilah" Bai saurareta ba yafice don yunwa ne ta isheshi cikin gyda yanufa yatarar da inna yaci yakoshi sannan yafice, fitansa kenan saiga yusuf wanda CID dayasaka su suka masa kwatance ya iso gydan, sallama yayi yashigo suka gaysa da inna wacce take zaune yadda yamata ladabi taji tana kaunarshi yatambayi ko aliya tananan, tace akaishi fanninta, aliya tamike kafafu batasan da shigowanshi ba hannu yasaka ya mintsineta, "innalilalh " tamike a razane wanda hakan yasa yayi murmushi, bata rai tayi kaman tunda aka halliceta batayi dariyaba tuni yasha jinin jikinsa, "meya faru don Allah?" Bata kulasa ba tamike tagyra jikinta tajawo gyale sannan ta yafa sannan tace "meye haka kashigowa mutane ba sallama, ko kamanta dakin mace ne?" Yayi mamakin magananta zaiyi magana tace "kafitamin kuma karka kara dawowa" baice komi ba kuma bai tashiba hakan yasa ta kwalawa idi kira, almajiri ne idi kato jibgege, hakan yasa yusuf naganinshi yamike jiki a sanyaye. Hakuri zakuyi yanzu azumi aka fara kadan kadan ne zaa ringa samu.

Godiya ga Benazir data rubuta wannan labarin.

To be continue on Wednesday insha Allah