Saturday 19 March 2016

Jinin Jikina Episode 3




“Jinin Jikina Episode 2


Isa ya muskuta ranshi yagama baci yamike yafice. Kuka Ali yasaka shikadai yasan abunda ke damunshi. Kokadan nadama bata ranshi don aganinshi abunda yakeyi shine daidai.
Wata rana nana tafito makaranta ali nabiye da ita. Wani mota ne ta tsaya daidai ali. Hakan yasa nanan tayi sauri gudun karma yaganta yamawa ali magananta. Don tafara gajiya da ganin kattan dasuke hawa kanta. Ta tsallake titi yayinda shikuma mai motar ya tsaya gun ali sukadanyi magana.
Can ya karaso gunta yana wani sham kamshi don tsabar iskanci meye nawucewa kibarni?. Tuni ta tsorata dashi. Ganin yanufo kanta dagudu tahau kan titi. Yana naaaana kisauko. Anma ina! Motar datake bayanta tuni tadaga da ita. Shikuwa gigice wa yayi yanufo kanta yafara balbale mai mota da masifa. Ibanda rashin lura yaza’ayi ka kadeta mai motan yafito wani saurayi fari kyakkyawa tuni yanufa kanta batare daya lura da abunda shi ali ke fada. Daukanta yayi zai sata motan. Juyin duniyannan yayi ali yariketa anma ina yagagara. Wasune suka taimaka acikin yan tsirarun mutanen dasuka taru don ganin meke faruwa. Aikuwa kafin ali ya hankara har mai motan yawuce. Tuni yatari mashin don yabishi. Traffic shi yarabasu haushi da takaici kaman yaci kanshi. Tayaya zaigane wani asibiti aka kaita? Kokuma wani guru zaije da ita?

Shikuwa tuki yakeyi duk hankalinsa atashe lallai yau idan yar mutane tamutu yazaiyi?. Asibiti yanufa tuni aka rufu akanta emergency akayi da ita. Addua yakeyi, zufa na kwaranya ajikinsa. Akalla bayan awa daya saiga likitan yafito tuni yace masa suna bukatar jini leda uku. Bashiri yace a debi nasa. Aka gwada jini aka ga yazo daya tuni aka deba . Shima aka bashi gadon don yahuta. Kwanan nana uku bata farfado shikuwa tuni yakira iyayensa yafada musu. Sunmasa jaje sosai. Tare da mata addua. Adaren ranan tafarka . Budewa nafarko bata fahimci a inda takeba. Sai can tadaga hannunta zata dora akai tuni taji zafi nan danan kuwa tayi yar kara. Dasauri yamike a tsaye yakaraso kanta. Sannu . Idonta tabude takaleshi. Akaro nafarko kenan daya mata asalin kallo. Lalle Allah yayi halitta anan. Dubi manyan ido agun yarinyanna. Shida zuciyarsa sai tadi sukeyi. Yadan muskuta tareda cewa barin kira miki Dr.  Yana fita yakira likitan suka shigi ajere. Nan likitan ya gwadata sannan yace. Abinci zataji tasha wadannan magungunan zata warke insha Allah. Nan yayita masa godiya.
Yafice yayinda shikuma yazauna yafara hada mata tea. Yahada mata mai kauri. Nana kuwa tsaf karantanshi takeyi. Itadai don kar ace tayi karyane anma dazatace bata taba ganin namiji mai kyau irinshiba. Yanda kasan shiya kera kanshi. Yazuba mata tare da dagowa yana cewa kisha zakiji dadi. Kawar dakanta tayi. Aikuwa tuni yagyara zama yafara lallami. Kinga kin rame kinyi kashin wuya. Duk kindawo wani iri. ‘Please i think u should take It’. Kallonsa take wow. Turancinsa ma yanda kasan balarabe irin yanda laravawa suke turanci. Tagirgiza kai. Can dai yarasa yazaiyi yace mekikeso?. Tayi shiru kamar bazata amsa ba can tace meye sunanka? Dago wa yayi yakalleta dakyau sannan yagyara zama yace sunana AHMED SULTAN. Anma abokai na sunfi kirana da sultan. Tayi shiru sannan tace uncle sultan. Baisan sanda ya kwashe da dariyaba. Noooo am not old. Just call me with my name please. Tadanyi murmushi sannan tace yaya sultan. Yayi murmushi saboda dadin daya ji yau ancemasa yaya kasancewarsa da tilo agun iyayensa. Yace naji dadin sunan. Takaleshi jiran yakarasa anma yayi tsit. Tadan muskuta zata gyara zama tare dacewa wash! Wayyo Allah! Dasauri yamike tare da gyara mata. Yahada mata tea da ferfesun kayan cikin tare da bata yana bata tana kurba yana bata tanacin ferfesu. Wasa wasa taci tas takoshi.
Yafita yanemo nurse tare da cemata bari yaje yadawo. Nurse ta taimaka mata tayi wanka tsaf. Yasiyo doguwar riga mai kyau daga gani yasha kudi tasaka tsaf. Ta bala’in yin kyau sosai. Nanda nan ramarta tafito anma tayi kyau. Ta kallabe dankwalinta tazauna agefen gadon. Nurse din tanemo mata sallaya ta tashi tabiya sallolin dake kanta. Ta idar kenan. Tashafa addua ta dade tana addua wa mahaifiyarta dakuma halin dasuke ciki. Takuma roki Allah yanuna mata mahaifiyarta anan kusa bada jimawa ba. Tashafa tare damikewa takoma kan gadon tazauna nurse din tamata sallama tafice. Minti kadan saiga sultan ya shigo. Yanemi gu yazauna tare dacewa sannu. Ta daga masa kai. Yace ina marar lafiyar take?. Tace wacce marar lafiya?. Yamike yabude kofa yagadai tabbas dakinne ba batan hanya yayiba? Yadawo yakura mata ido. Tabbas itace dama haka take da kyau?. Gabanshi ne yaketa faduwa. Dasauri yakira sunan Allah tare dacewa aiban ganekiba. Sannu yajikin. Murmushi tayi tare dacewa dasauki. Yace marar lafiya kinyi sallah? Tace sunana nana aisha abbakar turaki. Yakalleta dakyau sannan yace nice name.
 Akwai wani abokin babana abbakar turaki. Dasauri tace to bashi bane. ‘Ni babana ya rasu’. Dasauri yace oh am sorry Allah yajikansa! yamasa rahama ameen ameen. Tashare hawayenta don yatuna mata da rayuwarta. Hankalinsa yatashi don ganin hawayenta please dear meya sameki?. Batace komaiba. Nan yafara lallaminta. Har aka kira magrib yamike yaje yayi yadawo. Itama anan tayi. Bayan yazauna ne yace inaso kigayamin inda donginki suke donnasan hankalinsu atashe yake aduk inda suke kigayamin insanar musu kobahaka ba? Nanfa tafara sabon kuka tare dacewa banda kowa ni. Nan yaji tausayinta yace kiyi hakuri toh zankaiki gidanmu kizauna. Nan ta girgiza kai tare dacewa toh!.
Ali kuwa hankalinsa yayi dubu duk yatashi yanufi gida gun umma aikuwa yana zuwa yasameta yasanar da ita. Nan hankalinta yatashi tafara fada. Tana hawaye dama kanata nakasa rayuwan yarinyannan yanzu bukatarka tabiya kakashemin ya. Yanzu wayasan wanda yadauketa nagarine ko bata gari?. Kuka take sosai. Ali kuwa saibada hakuri. Baitaba dana sanin abinda ya aikataba harkuwa yanzu shi azuciyanci murnan barinta yakeyi bakin cikinsa daya ganin cewa bugeta akayi a mota baisan ko tasamu lafiya ko a a ba, anma yajima yana addua Allah ya nesantar da nana daga gareshi sanin halin dasuke ciki.

To be continue insha Allah next week…..
Godiya ga Binazzir






Feel Free To Comments Here...

No comments:

Post a Comment