Saturday 2 June 2018

Tuni yan kudu sun dawo daga rakiyar Buhari, sai dakikai daga Arewa- inji Sheikh Gumi


...yace idan gaskiya ne a dora Buhari da Shagari akan mizani aga waye mai gaskiya a cikinsu

DailyNigerian ta ruwaito fitaccen Malamin Addinin Musulunci a Najeriya, Sheikh Ahmad Gumi ya soki lamirin Gwamnatin Buhari kan batun yaki da cin hanci da rashawa. Shehun Malamin yayi wannan bayani ne a wajen Tafsirin Al-Kurani da yake gabatarwa a masallacin Sultan Bello.

Ya soki lamirin hukumar yaki da cin hanci da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa, musamman abinda suka yiwa tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Alhaji Mukhtar Ramalan Yero,inda aka makala masa wani allo dauke da sunan cewar shi mai laifi ne.

Sheikh Gumi yace, “Ina kan hanya zan taho wajen Tafseer din nan ne, aka tura min wani hoto dauke da tsohon Gwamnan Kaduna Ramalan Yero yana rike da wani allo da ya nuna cewar shi mai laifi ne”

“Wannan ba daidai bane, abinda suka yi masa kuskure ne, dole ne a garemu mu gaya musu gaskiya”

“Da ya kamata Ramalan Yero ya jefar da allon yaki yadda ya daga, ba abinda zai faru in yayi haka, domin kotu ce kadai ke da ikon kama mutum da laifi”

“Batun Demokaradiyyar da ake magana, karya ake yi, domin ana take hakkin mutane”

“Idan ba dan an yafewa Shugaba Buhari laifukansa ba, da ba zai sake zama Shugaban Najeriya ba”

“Idan gaskiya ne a dora Buhari da Shagari akan mizani aga waye mai gaskiya a cikinsu”

No comments:

Post a Comment