Tuesday 5 June 2018

Gwamnatin Jonathan ba ta yi kama karya irin ta wannan Gwamnain ba – inji Dakta Gumi

Daga DailyNigerian Hausa

Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan,Sheikh Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya caccaki rundunar ‘yan sanda ta kasa kan yadda suka ci zarafin Shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki. A cewarsa cin fuska ne ‘yan sanda su gayyace shi maimakon su je su same shi.

Mutum na uku a kasar nan yana da matukar muhimmanci kwarai da gaske, bai kamata ba kuma a wulakanta shi ba, irin yadda ‘yan sanda suke yi masa yanzu haka. Idan Shugaban kasa ya bari aka wulakanta shi, to ya sani kansa ya wulakanta”

“Idan aka dore a haka, to, shima Shugaban kasa duk ranar da ya sauka haka zai kare ba shi da kima, ana iya sanya ‘yan sanda su kama shi ko su wulakanta shi babu kuma abinda zai faru”

“Me yasa ake tsare da Sambo Dasuki, ku gaya mana a lokacin Gwamnatin Jonathan da ta gabata an yihaka ne? Amma me yasa yanzu ake yiwa mutane bitada da kulli bayan a zamanin gwamnatin Jonathan sam bamu shaidi hakan ba”

No comments:

Post a Comment