Tuesday 5 June 2018

Tsuguno bata karewa Dino Malaye ba za'a cigaba da gurfanar dashi gaban Kotu


Tunda Dino Melaye ya samu lafiya, a cigaba da gurfanarsa – AGF Malami ya bukaci kotu

Naijdotcom ta ruwaito Ministan Shari’a kuma babban lauyan tarayya, Abubakar Malami, ya bukaci babban kotun birnin tarayya Abuja, da ta cigaba da gurfanar da Sanata Dino Melaye, bayan dakatad da sanadiyar jinya da yake yi.

Jaridar Punch ta bada rahoto a jiya Litinin cewa ta samu wasikan da aka turawa kotu tana sanar da ita cewa Dino Melaye ya samu lafiya har ya koma bakin aiki a majalisar dattawa ranan30 ga watan Mayu.

Ofishin babban lauyan kasa tana tuhumar Dino Melaye da karya ga hukumar yan sanda domin yiwa na kusa da gwamnan jihar Kogi, Edward Onoja David, sharri cewa ya tura wasu kashe shi.

A ranan 17 ga watan Mayu 2018, Justice Olasunbo Goodluck, ya dakatad da karar Melaye ne zuwa lokacin da za’a sallameshi daga babban asibitin tarayya da ke Abuja inda yake kwance.

A wasikar, lauyan gwamnati, Mr Shuaibu Labara, ya laburtawa kotu cewa an salami Melaye kuma ya koma bakin aiki rike da sanda da abu a wuya.

Tunda ya koma kuma, an ganshi yana magana a majalisa saboda haka, kotu ta bada sabon ranan domin cigaba da gurfanarsa.

No comments:

Post a Comment