Tuesday 5 June 2018

Sanatoci da yan majalisar dokoki sun yanke shawarar tsige Buhari muddin bai cika sharudda 10 ba

DA DUMI DUMI: Sanatoci da yan majalisar dokoki sun yanke shawarar tsige Buhari muddin bai cika sharudda 10 ba

Naij.com ta ruwaito Yan majalisan wakilai da dattawa sun lashi takobin tsige shugaba Muhamadu Buhari face ya cika wasu sharruda goma da suka kindaya masa.

Bayan ganawar da yan majalisan sukayi a yau wanda ya kwashe akalla sa’o’I 4, yan majalisan sun yanke shawaran cewa za su tsige shugaban da karfinsu idan har bai cika wadannan sharruda 10 ba.

Sharrudan sune,:

1. A baiwa hukumomin tsaro umurnin kawo karshen kashe-kashen da ke faruwa a fadin kasa.

2. Cin mutuncin yan adawan da fadar shugaban kasa keyi ya isa hakan kuma kada ya sake faruwa

3. Wajibi ne bangaren zantarwa su bi doka

4. Za’a daurawa shugaban kawa alhakin dukkan abinda wadanda ya nada suka yi

5. Gwamnatin tarayya ta nuna gaskiya wajen yaki da rashawan da takeyi

6. Wajibi ne a karewa majalisar dokoki hakkinsu kuma ayi binciken wadanda suka sace sandar majalisa

7. Majalisar dokoki za ta hada kai da majalisar ECOWAS, EU,UN da yan kungiyoyin fafutuka wajen kare demokradiyyan Najeriya

8. Wajibi ne a kawo karshen rashin aikin yi a Najeriya

9. Wajibi ne a ja kunne kuma a caccaki sifeto janar na hukumar yan sanda

10. Wajibi ne a jinjinawa shugaban majalisan dattawa, Bukola Saraki da kuma kakakin wakilai, Yakubu Dogara.

Yan majalisan sunce face an cika wadannan sharruda, ba zasu dagawa bangaren shugaban kasa kafa ba.

No comments:

Post a Comment