Monday 11 June 2018

Shugaba Buhari Da Sarkin Moroco Sun Kulla Alaka Kan Harkokin Man Fetur, Gas Da Sauransu

Shugabannin biyu sun tattauna da kuma cimma yarjejeniya na karfara tattalin arzikin kasashen biyu.

Wadanda suka rattaba hannu kan wannan yarjejeniya sune Manaja a kamfanin NNPC, Mr Farouq da kuma ministan man kasar Moroco, Misis Amina Benkhadra

Haka kuma shugaba Muhammadu Buhari da Sarki Muhammad VI sun shaida yarjejeniyar gina babban masana’antar hada sinadarin takin zamani wato Ammonia, wanda shugaban sanya hannun jarin Nijeriya, Mista Uche Orji da Mista Mostafa Terrab na Moroco suka rattaba hannu.

No comments:

Post a Comment