Friday 8 June 2018

Tsaffin ‘yan sabuwar PDP zasu fice daga APC 23 ga watan Yuni

Wata majiya mai tushe ta shaidawa gidan jaridar DAILY TRUST cewar nan da ranar 23 ga watan Yuni tsaffin ‘yan sabuwar PDP da suka hada da SHugaban majalisar dattawa dBukola Saraki da kakakin majalisar wakilai na tarayya Yakubu Dogara zasu fice daga jam’iyyar APC zuwa wata jam’iyya.

Tsaffin ‘yan sabuwar PDP din sun zabi ranar 23 ga watan Yuni ne, domin ta zamo daidai da ranar da jam’iyyar APC zata yi babban taron ta na kasa inda zata zabi sabbin Shugabanni.

Majiyar ta shaidawajaridar cewar jiga jigan jam’iyyar sun gama tattara komatsansu domin ficewa daga jam’iyyar ta APC domin tsallakawa zuwa jam’iyyar adawa wanda suke karkashin jagorancin Alhaji Kawu Baraje.

Idan har ta tabbata tsaffin ‘yan sabuwar PDP zasu fice daga jam’iyyar APC a ranar babban taron jam’iyyar na kasa, to, tarihi zai maimaita kansa. Domin a shekarar 2013 ne tsohon mataimakin Shugaban kasa Atiku Abubakar ya jagoranci wasu Gwamnoni da mukarraban PDP suka ficee daga jam’iyyar a lokacin da jam’iyyar ke yin babban taron ta na kasa.

Inda bayan ficewarsu daga jam’iyyar PDP suka hallara a Shehu YarAdua santa inda suka bayyana kansu a matsayin sabuwar PDP, karkashin jagorancin Alhaji Kawu Baraje wanda ya jagorance su a lokacin.

Ficewar da tsaffin ‘yan sabuwar PDP suka yi daga jam’iyyar tasu, na daga cikin dalilan da suka sabbabawa jam’iyyar ta PDP samun koma baya tare kuma da faduwa babban zaben shekarar 2015.

No comments:

Post a Comment