Tuesday 12 June 2018

Shugaba Buhari ya yabi matasan Najeriya a ganawar da yayi da firaiministan Morocco

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya gana da firaministan kasar Morocco, Saadeddine Othmani, inda ya shaida mishi cewa mutanen Najeriya, wanda yawancin su matasa ne suna da kokarin aiki tukuru duk inda suka samu kansu a gida Najeriya ko a kasashen waje.

Shugaba Buhari ya kara da cewa shi yasa gwamnatin shi take kokarin ganin ta tallafawa matasan dan su bayar da gudummuwar data dace wajan ciyar da kasar gaba,

Ya kara da cewa Najeriya na kokarin ganin ta inganta harkokin Ilimi dana noma ta hanyar yin hadaka da kasashen Duniya wajan tabbatar da hakan.

Ya bayyana cewa an samu raguwar shigar da shinkafa kasar sosai, sannan kuma hadin gwiwar da Najeriya tayi da kasar Moroccon yasa kudin takin zamani ya ragu da kashi hamsin cikin dari.

Da yake jawabi a ganawar tasu, Firaiminista, Saadeddine ya bayyana cewa 'yan Morocco sun tabbatar da 'yan Najeriya nada hazaka dan sun gani a kasa, sannan kuma zasu cigaba da tabbatar da dangantaka me kyau da Najeriya.

Shugaba Buhari ya kuma gana da shugaban masu bayar da shawara akan harkar kasuwanci na kasar ta Morocco Ben Chemmas da kuma shugaban majalisar wakilai Habib El-Malki.

No comments:

Post a Comment