Tuesday 5 June 2018

Anci zarafin addinin Musulunci a wakar Shaku Shaku – MURIC


Daga DailyNigerian Hausa

*Wakar fitsarar da aka ci zarafin addinin Musulunci*

Wani mawaki da ake kira da sunan Folarin Falana ko inkiya (Falz the Bahd Guy) ya fitar da wata sabuwar waka mai suna Shaku Shaku da yaci zarafin Fulani da kuma addinin Musulunci a cikinta.

A cikin faifan bidiyon wakar an nuna wani Bafulatani yana sare kan mutane babu gaira babu dalili, abinda yake nuna cin zarafi ga kabilar Fulani a Najeriya. haka kuma a cikin akar an ci zarafin addinin Musulunci, inda aka nuna wata mata sanye da Hijabi tana rawar ‘yan kwaya.

Wakar dai an sanya mata sunan “This is Nigeria” ma’ana “Wannan ita ce Najeriya” inda a cikin wakar aka dinga wata rawa ta rashin mutunci da aka sanya sunan shaku shaku.

A sabpda haka ne itacciyar kungiyar kare ‘yancin Musulmi ta MURIC ta yi Allawadai da wannan sabon faifan bidiyo da ya ci zarafin Musulmi, ta nemi kuma a gaggauta janye wakar daga kasuwa matukar ana son zaman lafiya.

No comments:

Post a Comment