Friday 20 April 2018

Hukumar 'Yan Sanda Ta Yi Wa Magu Karin Girma

Hukumar 'yan sanda ta kasa, a yau Juma'a ta sanar da karin girma ga manyan jami'an 'yan sanda 18.

Shugaban hukumar EFCC, Ibrahim Magu na daga cikin wadanda aka karawa girman.

Hukumar ta kara masa girma ne daga matsayin mataimakin kwamishanan 'yan sanda zuwa kwamishana.

Idan za a iya tunawa, shugaba Muhammadu Buhari ya nada Ibrahim Magu a matsayin shugaban hukumar EFCC domin yaki da cin hanci da rashawa. Amma duk da hakan, majalisar dattawa ta ki tabbatar da shi bisa wasu dalilai nasu.

Wannan sabon karin girma da aka yi wa su Magu,na kunshe ne cikin jawabin kakakin hukumar ta 'yan sanda, Ikechukwu Ani.

No comments:

Post a Comment