Thursday 19 April 2018

Mutane Da Yawa Ba Su Fahimci Kalaman Shugaba Buhari Ba, Musamman Wasu 'Yan Arewa

Daga Comrade Affan Buba Abuya Gombe

Abun da Buhari yake nufi a fahimta ta, Matasa da yawa a yankin da ake tono mai suna zaman jiran a ba su kudi ba tare da sun yi aikin komai ba saboda a yankin su ake tono mai kamar yadda yanzu haka ake kashe biliyoyin kudi a wannan yanki ga wadanda basa aikin komai ba sa yiwa kasa wani katabus.

Da yawan su matasa ne masu zaman banza kuma ko karatu ba suyi ba, jira sukeyi a basu kuma wannan hali ba zai taba daurewa ba, ba zai taimaki tattalin arzikin kasa ba da rayuwar matasa a gaba.

Domin tabbatar da haka kaje garin ku cikin anguwanku zakaga yanda matasa suke zaman banza, ba karatu, ba sana’a kuma suna so suyi kudi sai KJK da shaye shaye da zama yan kalare sukeyi ko sara suka wasu gurbatattu suna amfani dasu a siyasa.

Muna tare da kalaman Shugaban Kasa Buhari, Allah ya shiryar mana da matasan mu.

No comments:

Post a Comment