Friday 27 April 2018

Manoman Jihar Neja Ta Arewa Sun Samu Horo Akan Dabarun Noma Na Zamani

Taron bita da karawa juna sani akan sabbin hanyoyin dabarun noma na zamani ga manoman yankin Neja ta Arewa da sanata mai wakiltar Jihar Neja ta Arewa kuma mai magana da yawun majalisar dattijan Najeriya Dr. Aliyu Sabi Abdullahi (Baraden Borgu) ya shiryawa manomar yankinsa tare da hadin guiwar hukumar bunkasa harkar noma na jami'ar Obafemi Awolowo.

Taron bitar na yini biyu da ya gudana a dakin taro na hukumar gidan gona na Kontagora yasamu halartar manoma daga kananan hukumomi 8 dake yankin inda manyan masana harkar noma daga jami'ar Obafemi Awolowo suka gabatar da lakcoci daban-daban ga manoman, tare da koyarwa na zahiri ga manoman.

Hakazalika anbaiwa manoman tallafin irin masara da dawa na zamani tare da tallafin naira dubu ashirin da hudu ga wadanda suka halarci bitan domin bunkasa harkar noma a yankin Neja ta Arewa da Kasa baki daya.

Ko a shekarar da ta gaba ta ya dauki nauyin shirin karawa juna ilimi ga malammai 125 wanda ya gudana a Safara Motel Kontagora tare da basu tallafin naira dubu talatin-talatin, sannan a wannan shekarar ya dauki nauyin karawa juna sani ga malamai 130 wanda ya gudana a garin New Bussa tare da basu tallafin dubu talatin talatin.

Bayan haka shirya shirin bada taffalin jarin sana'o'i na musamman ga mata 95 wanda ya gudana a Safara Motel Kontagora tare da basu tallafin naira dubu talatin-talatin, hakazalika ya sake shirya makamancin wannan horas wa a garin New Bussa.

Bangaren matasa ya daukin nauyin horar da matasa 100 daga kananan hukumomi 8 dake yankin sa a kwalejin koyon kiwon kifi tare da basu tallafi.

No comments:

Post a Comment