Tuesday 29 May 2018

Al'ummar Jihar Bauchi Sun Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Tazarcen Gwamna M.A A Zaben 2019

Al'ummar Jihar Bauchi Sun Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Tazarcen Gwamna M.A A Zaben 2019

Dandazon al'umma a jihar Bauchi wadanda suka hada maza da mata a jiya Litinin sun yi gangami zuwa fadar gwamnatin jihar domin nuna goyon bayan su ga gwamna Barista M.A Abubakar, inda suka jaddada cewa ba su da wani dan takara da ya wuce gwamnan M.A a zaben 2019.

A yayin jin ta bakin jagoran gangamin, Kabir G. Kobi Dan Hajiya, ya bayyana cewa sun yi gangamin ne domin kara jaddada goyon bayan su ga Maigirma Gwamnan Jihar Bauchi, Barista Mohammed Abdullahi Abubakar.

Da yawa daga cikin masu zanga-zangar sun bayyana cewa kasancewar sun gamsu da salon mulkin Barista M.A, babu abin da zai sanya su juya masa baya a zaben 2019.

No comments:

Post a Comment