Sunday 27 May 2018

Gidaje Fiye Da 100 Sun Ruguje Sakamakon Guguwa Mai Karfi A Karamar Hukumar Gumel Dake Jihar Jigawa

Gidaje Fiye Da 100 Sun Ruguje Sakamakon Guguwa Mai Karfi A Karamar Hukumar Gumel Dake Jihar Jigawa

Sakamakon Guguwa Mai Karfin Gaske Yayi Sanadiyar Rugujewar Gidaje Fiye Da Dari A Cikin Unguwar Dan Tanoma Dake  Garin Gumel  Jihar Jigawa.

Tuni Shugaban Karamar Hukumar Gumel Hon. Aminu Sani Gumel  Ya Tura Wakilci Daga Majalissar Zartawa Karamar Hukumar Gumel Domin Duba Irin Barnar Da Guguwar Tayi, Tare Da Jajantawa Al'umma Da Iftila'i Ya Samesu.

Shugaban Karamar Hukumar Yayi Matukar Jimami,Da Nuna Damuwarsa,Ganin Yadda Iskar Ta Shafi  Sama Da Gidaje Dari.

A Karshe Cikin Alhini, Karamar Hukumar Gumel Ta Jajantawa Al'ummar Da Abin Ya Shafa,Tare Da Kira a Gare Su Cewa Su Dauki  Wannan A Matsayin Wata Jarraba Daga Ubangiji.

Sannan Karamar Hukumar Gumel Karkashin Jagorancin Za6a66en Ciyaman Hon Aminu Sani  Tayi  Alkawarta,Cewa Insha Allahu Zatayi Bakin Kokarinta  Domin Mika Al'amarin Ga Hukumar Agajin Gaggawa Ta Jaha,Domin Kawo Musu Tallafin Gaggawa.

No comments:

Post a Comment