Sunday 27 May 2018

PDP ce ta tsiyatar da Najeriya,- Oshomole

Tsohon gwamnan jihar Edo, Kwamared Adams Oshiomole ya sake yiwa gwamnatin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan shagube inda ya ce idan da za'a rabawa dukkan 'yan Najeriya kudaden da ake zargin gwamnatin Jonathan ta karkakatar ,da kowa ya zama attajiri a kasar.

Tun a baya, Oshiomole ya dade yana cacakar gwamnatin Jonathan a kan zargin karkatar da kudaden Najeriya.

Oshiomole ya yi wannan furuci ne a jiya Juma'a yayin da ya ke jawabi ga shugabanin jam'iyyar APC na jihar Edo.

Yace ,Aljihun kowane 'dan Najeriya zai cika ya batse idan da za'a raba musu kudaden da aka karkatar zamanin Jonathan

Osjomole ya ce ,dole ne a rika jaddada irin mulkin da gwamnatin PDP ta kwashe shekaru 16 tana yi wanda hakanne ya jefa Najeriya cikin talauci da fatara.

Ya ce jam'iyyar APC a karkashin jagorancin shugaba Muhammadu Buhari tana kokorin ceto yan Najeriya daga cikin halin kuncin da PDP ta jefa kasar.

"Hakkin hakkinmu ne mu magoya bayan jam'iyya mu fadakar da mutanen karkara wadanda suka jefa mu irin halin da muka shiga a yau da kuma kokarin da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari keyi don ceto mu, wanda hakan yasa yan Najeriya a yanzu sun fara alfahari da kasar," inji Oshiomole.

Tsohon gwamnan ya cigaba da cewa ya kamata mutane su fahimci irin wahalar da ke tattare da yin gyara a gidan daya ruguje saboda daura turbar sabon gini da kammala ginin ba abu ne da za'a iya kammalawa a dare daya ba.

A cikin yan kwanakin nan ne Oshiomole ya nuna sha'awarsa na tsayawa takarar kujerar shugabancin jam'iyyar APC inda kuma ya kara da cewa shugaba Buhari ne zai lashe zabe saboda irin nasarorin da ya samu a yanzu.

No comments:

Post a Comment