Thursday 24 May 2018

Za A Rusa Gidajen Karuwai Da Na Barasa A Jihar Borno

Gwamnan Jihar Borno Alh Kashim Shettima, ya bada wa'adin kwanaki 10 da a rusa gidan karuwai da wajen holewanan na Galadima dake garin Maiduguri.

Galadima mattara ce ta karuwai, mashaya da sauran lalatattu masu aikata badala da bata tarbiyar al'umma.

Su ma manyan Malaman musulunci na jihar sun sha jan hankalin gwamnati dangane da wannan wuri.

Wannan umurnin ya zo ne kwanki kadan bayan da Gwamna Shettima ya bada dokar korar 'yan cacar NAIJABET a fadin jiharsa.

Daga Comr Mohammed Pulka

No comments:

Post a Comment